Home Taska Sojojin Najeriya Sun Hallaka Kwamandojin ISWAP a Sambisa

Sojojin Najeriya Sun Hallaka Kwamandojin ISWAP a Sambisa

Sojojin Najeriya Sun Hallaka Kwamandojin ISWAP a Sambisa

Rahotanni a Najeriya sun ce sojojin Najeriya sun halaka wasu kwamandojin Iswap a Sambisa ciki har da wanda ake kira Amir Buba Danfulani wanda ake zargin ya shigar da fulani makiyaya ƙungiyar.

A cikin rahoton da ta fitar, jaridar PRNigeria da ke da kusanci da rundunar sojin Najeriya ta ce an yi wa mayaƙan ne luguden wuta ta sama a wasu sansanoninsu da kuma dajin Sambisa a arewa maso gabashin Najeriya, kamar yadda majiyoyin soji suka tabbatar.

Sai dai babu wata sanarwa kawo yanzu daga rundunar sojin Najeriya da ke tabbatar da al’amarin.

Rahotannin sun ce an yi wa mayaƙan ne ruwan rokoki a Tumbun Kaiyowa da kuma Tumbun Allura, tare da kashe mayaƙan.

An kuma yi wa mayaƙan ruwan wuta ta sama a dajin Sambisa. Kwamandojin Iswap da aka kashe sun hada da Musa Amir Jaish da Mahd Maluma da Abu-Ubaida da Abu-Hamza da kuma Abu-Nura umarun Leni, a cewar PRNigeria.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp