Home SIYASA Wike da Masu Ruwa da Tsaki na PDP Sun yi Taro

Wike da Masu Ruwa da Tsaki na PDP Sun yi Taro

Wike

Wike da Masu Ruwa da Tsaki na PDP Sun yi Taro

 

SIYASA – Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya kira taron shugabanni da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP a jihar.

Taron dai shi ne na farko a jihar tun bayan zaben fidda gwani na shugaban kasa da kuma rikicin da ya biyo bayan sakamakon ta.

Ko da yake ba a iya gano ajandar taron ba, wata majiya ta shaida wa wakilin PUNCH cewa tun bayan abubuwan da suka faru a jam’iyyar a matakin kasa har yanzu masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a jihar ba su ji ta bakin gwamnan ba.

Don haka ana sa ran masu ruwa da tsaki za su ji ta bakin gwamnan kai tsaye kan matsayinsa da kuma matakin da za a dauka na gaba dangane da rikicin PDP.

Wadanda ake sa ran a taron sun hada da shugabannin jam’iyyar, ‘yan majalisar zartarwa na jiha, shugabannin kananan hukumomin jam’iyyar da sauran zababbun wasu.

Majiyar ta ce taron mai muhimmanci yana da nasaba da rikicin da ya barke a jam’iyyar a kwanakin baya, domin gwamnan zai yi wa mutanensa bayanin matsayin da tawagarsa ta dauka na ficewa daga majalisar yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar.

Wannan na zuwa ne gabanin wani taron manema labarai da aka shirya yi a safiyar Juma’a 23 ga watan Satumba, 2022, wanda Gwamna Wike zai yi jawabi a gidan gwamnati dake Fatakwal.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp