Home SIYASA Wike da Masu Ruwa da Tsaki na PDP Sun yi Taro

Wike da Masu Ruwa da Tsaki na PDP Sun yi Taro

Wike

Wike da Masu Ruwa da Tsaki na PDP Sun yi Taro

 

SIYASA – Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya kira taron shugabanni da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP a jihar.

Taron dai shi ne na farko a jihar tun bayan zaben fidda gwani na shugaban kasa da kuma rikicin da ya biyo bayan sakamakon ta.

Ko da yake ba a iya gano ajandar taron ba, wata majiya ta shaida wa wakilin PUNCH cewa tun bayan abubuwan da suka faru a jam’iyyar a matakin kasa har yanzu masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a jihar ba su ji ta bakin gwamnan ba.

Don haka ana sa ran masu ruwa da tsaki za su ji ta bakin gwamnan kai tsaye kan matsayinsa da kuma matakin da za a dauka na gaba dangane da rikicin PDP.

Wadanda ake sa ran a taron sun hada da shugabannin jam’iyyar, ‘yan majalisar zartarwa na jiha, shugabannin kananan hukumomin jam’iyyar da sauran zababbun wasu.

Majiyar ta ce taron mai muhimmanci yana da nasaba da rikicin da ya barke a jam’iyyar a kwanakin baya, domin gwamnan zai yi wa mutanensa bayanin matsayin da tawagarsa ta dauka na ficewa daga majalisar yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar.

Wannan na zuwa ne gabanin wani taron manema labarai da aka shirya yi a safiyar Juma’a 23 ga watan Satumba, 2022, wanda Gwamna Wike zai yi jawabi a gidan gwamnati dake Fatakwal.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp