Home SIYASA INEC ta bai wa Hon. Alhassan Ado Doguwa shaidar sake cin zaɓe

INEC ta bai wa Hon. Alhassan Ado Doguwa shaidar sake cin zaɓe

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya ta bai wa Hon. Alhassan Ado Doguwa shaidar sake cin zaɓe a matsayin ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar tarayya ta Doguwa da Tudun Wada, daga Jihar Kano.

Karo na shida kenan, da Ɗan Majalisar na tarayya ke samun nasarar zuwa majalisar ta wakilai daga Jihar Kano, da ke Arewa Maso Yammacin Najeriya, tun bayan dawowar mulkin dimokraɗiyya a Najeriyar a cikin shekarar 1999.

Tun da farko dai hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙara (INEC) ta soke nasarar Da Hon. Alhassan Ado Doguwa ya samu, a zaɓen 25 ga watan Fabrairu, saboda jami’in sanar da sakamakon, Farfesa Ibrahim Adamu Yakasai ya ce “tursasa masa” aka yi.

Sai dai, jami’in sanar da sakamakon a zaɓen cike-giɓi na mazaɓar, Farfesa Sani Ibrahim a ranar 15 ga watan Afrilu, ya bayyana Alhassan Doguwa Doguwa a matsayin wanda ya yi nasara da ƙuri’u 41,572 bayan wannan zaɓen lafiya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp