Home Taska Ana Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14

Ana Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14

Ana Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14

 

Ana zargin mayaƙan Boko Haram da kashe sojojin Nijar 14 tare da jikkata wasu da dama a garin N’Guigmi da ke yankin Diffa a kudu maso gabashin ƙasar, kamar yadda shafin Actu Niger mai zaman kansa ya ruwaito.

Rahoton ya ce, bisa bayanan da aka samu daga mazauna yankin, maharan ɗauke da manyan makamai sun kai hari ne da misalin ƙarfe 9:00 na safe a ranar 31 ga Yuli, inda suka farmaki sansanin jami’an tsaro da ke wajen garin N’Guigmi a yankin Diffa.

An binne sojojin da aka kashe a wannan rana da yamma, a wani taro da Gwamnan Diffa, Manjo Janar Mahamadou Ibrahim Bagadoma, ya halarta, inda ya isar da saƙon ta’aziyyar manyan shugabannin Nijar ga iyalan mamatan tare da ƙarfafa gwiwar sojojin da ke bakin aiki.

Rahoton ya ƙara da cewa harin ya jawo martani mai ƙarfi daga dakarun Nijar, waɗanda suka ƙaddamar da farmakin ramuwar gayya domin daƙile maharan.

Sojojin sun ce sun kashe wasu daga cikin maharan, sannan suka fara wani samame da sintiri domin bibiyar sauran waɗanda suka tsere a yankin Tafkin Chadi, inda suka ce sun daɗe suna haddasa tashe-tashen hankula.

Yankin Diffa, wanda ke iyaka da Chadi a gabas da Najeriya a kudu, ya kasance ɗaya daga cikin wuraren da suka fi fama da hare-haren Boko Haram tun bayan da rikicin ya bazu zuwa Nijar a shekarar 2015.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp