Ana Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14
Ana zargin mayaƙan Boko Haram da kashe sojojin Nijar 14 tare da jikkata wasu da dama a garin N’Guigmi da ke yankin Diffa a kudu maso gabashin ƙasar, kamar yadda shafin Actu Niger mai zaman kansa ya ruwaito.
Rahoton ya ce, bisa bayanan da aka samu daga mazauna yankin, maharan ɗauke da manyan makamai sun kai hari ne da misalin ƙarfe 9:00 na safe a ranar 31 ga Yuli, inda suka farmaki sansanin jami’an tsaro da ke wajen garin N’Guigmi a yankin Diffa.
Read Also:
An binne sojojin da aka kashe a wannan rana da yamma, a wani taro da Gwamnan Diffa, Manjo Janar Mahamadou Ibrahim Bagadoma, ya halarta, inda ya isar da saƙon ta’aziyyar manyan shugabannin Nijar ga iyalan mamatan tare da ƙarfafa gwiwar sojojin da ke bakin aiki.
Rahoton ya ƙara da cewa harin ya jawo martani mai ƙarfi daga dakarun Nijar, waɗanda suka ƙaddamar da farmakin ramuwar gayya domin daƙile maharan.
Sojojin sun ce sun kashe wasu daga cikin maharan, sannan suka fara wani samame da sintiri domin bibiyar sauran waɗanda suka tsere a yankin Tafkin Chadi, inda suka ce sun daɗe suna haddasa tashe-tashen hankula.
Yankin Diffa, wanda ke iyaka da Chadi a gabas da Najeriya a kudu, ya kasance ɗaya daga cikin wuraren da suka fi fama da hare-haren Boko Haram tun bayan da rikicin ya bazu zuwa Nijar a shekarar 2015.










