Iyanen Babban Jami’in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga Sojoji
Rundunar sojin Najeriya ta ce matar babban jami’in kula da harkokin kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP tare da ɗanta mai shekara 11 sun miƙa wuya ga dakarunta na Operation Hadin Kai ta ƙauyen Kusuma da ke Jihar Borno.
Read Also:
Sojojin sun ce binciken farko ya nuna cewa mijin matar, wanda ya kasance babban kwamandan ISWAP ya miƙa wuya a ranar 25 ga Yuli kuma shi ne ya umarce ta da ta fito daga maɓoyarsu tare da ɗansu.
Sanarwar sojojin ta ce mayaƙan sun tsere a wani samame ta daban da sojojin suka kai a yankin Turoh bayan samun bayanan sirri.
Bayan binciken yankin, dakarun sun kwato babura biyu da kuma tarin miyagun ƙwayoyi da mayaƙan suka bari a baya, yayin da rundunar ta ce za ta ci gaba da ƙarfafa hare-haren da suka dogara da sahihan bayanan sirri.












