Home Labarai Hukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗe

Hukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗe

Hukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗe

 

Babbar Kotun Jihar Akwa Ibom, ta yanke wa wani direban Keke Napep, Michael Effiong Japhet, hukuncin ɗaurin rai da rai bayan ta same shi da laifin aikata fyaɗe da kuma sata.

Mai shari’a Archibong Archibong, ya ce kotun ta gamsu da hujjojin da masu gabatar da ƙara suka bayar, inda ta tabbatar da cewa Japhet ya aikata laifukan da ake zargin sa da aikatawa.

Kotun ta yanke masa hukuncin ne bisa dokar laifukan fyaɗe ta Jihar Akwa Ibom ta shekarar 2000, bayan an same shi da laifin yi wa wata mata fyaɗe da kuma ƙwace mata kuɗi.

An bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar 23 ga watan Fabrairun 2015, lokacin da Japhet ya ɗauki wata mai sayar da kayan marmari daga Ekom Iman zuwa Iko Ofon a Ƙaramar Hukumar Ikono.

A maimakon kai ta inda ta nufa, an ce ya sauya hanya ya bi da ita zuwa wani waje da ba kowa, inda ya yi mata fyaɗe.

An kuma zarge shi da ƙwace jakarta mai ɗauke da kuɗin cinikinta na ranar Naira 7,000, duk da roƙon sa da ta yi kada ya cutar da ita.

Kotun ta ce bayan sauraron dukkanin shaidun, ta samu Japhet da laifin da ake tuhumarsa da shi, sannan ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai da rai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga PantamiGazawar Demarketing: Yadda Sukar Rarara Mai Cike da Kiyayya ga Pantami Ya Rushe Daga Yushau A. ShuaibƘungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin AikiDakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da suƳan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari'a da ke Jihar KatsinaBa ma Goyon Bayan a Riƙa Tura Sojoji Domin Aikin Tsaro a Lokacin Zaɓe - INECJam'iyyar NDC ta Buƙaci Sanata Hanga da Gaya da su Sake Tunani Kan Sauya SheƙaYan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata MatarsaMutane 15 Sun Mutu a Sabon Harin Yan Bindiga a Jihar Benue Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi MataimakinsaJami'an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu a Jihar Sokoto 
X whatsapp