Home Labarai Hukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗe

Hukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗe

Hukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗe

 

Babbar Kotun Jihar Akwa Ibom, ta yanke wa wani direban Keke Napep, Michael Effiong Japhet, hukuncin ɗaurin rai da rai bayan ta same shi da laifin aikata fyaɗe da kuma sata.

Mai shari’a Archibong Archibong, ya ce kotun ta gamsu da hujjojin da masu gabatar da ƙara suka bayar, inda ta tabbatar da cewa Japhet ya aikata laifukan da ake zargin sa da aikatawa.

Kotun ta yanke masa hukuncin ne bisa dokar laifukan fyaɗe ta Jihar Akwa Ibom ta shekarar 2000, bayan an same shi da laifin yi wa wata mata fyaɗe da kuma ƙwace mata kuɗi.

An bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar 23 ga watan Fabrairun 2015, lokacin da Japhet ya ɗauki wata mai sayar da kayan marmari daga Ekom Iman zuwa Iko Ofon a Ƙaramar Hukumar Ikono.

A maimakon kai ta inda ta nufa, an ce ya sauya hanya ya bi da ita zuwa wani waje da ba kowa, inda ya yi mata fyaɗe.

An kuma zarge shi da ƙwace jakarta mai ɗauke da kuɗin cinikinta na ranar Naira 7,000, duk da roƙon sa da ta yi kada ya cutar da ita.

Kotun ta ce bayan sauraron dukkanin shaidun, ta samu Japhet da laifin da ake tuhumarsa da shi, sannan ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai da rai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp