Home Labarai Hukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗe

Hukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗe

Hukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗe

 

Babbar Kotun Jihar Akwa Ibom, ta yanke wa wani direban Keke Napep, Michael Effiong Japhet, hukuncin ɗaurin rai da rai bayan ta same shi da laifin aikata fyaɗe da kuma sata.

Mai shari’a Archibong Archibong, ya ce kotun ta gamsu da hujjojin da masu gabatar da ƙara suka bayar, inda ta tabbatar da cewa Japhet ya aikata laifukan da ake zargin sa da aikatawa.

Kotun ta yanke masa hukuncin ne bisa dokar laifukan fyaɗe ta Jihar Akwa Ibom ta shekarar 2000, bayan an same shi da laifin yi wa wata mata fyaɗe da kuma ƙwace mata kuɗi.

An bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar 23 ga watan Fabrairun 2015, lokacin da Japhet ya ɗauki wata mai sayar da kayan marmari daga Ekom Iman zuwa Iko Ofon a Ƙaramar Hukumar Ikono.

A maimakon kai ta inda ta nufa, an ce ya sauya hanya ya bi da ita zuwa wani waje da ba kowa, inda ya yi mata fyaɗe.

An kuma zarge shi da ƙwace jakarta mai ɗauke da kuɗin cinikinta na ranar Naira 7,000, duk da roƙon sa da ta yi kada ya cutar da ita.

Kotun ta ce bayan sauraron dukkanin shaidun, ta samu Japhet da laifin da ake tuhumarsa da shi, sannan ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai da rai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 2 Sun Mutu Bayan Hatsarin Tankar Mai a IbadanƘungiyar MURIC ta Zargi INEC da Hana Mata Masu Hijabi Kaɗa ƙuri’arsu a Zaɓen Jihar Osun Babu Dan Takara ko Tikiti da zai iya Doke Namu a Zaɓen 2027 - Kwankwaso Mutane 5 Sun Mutu Bayan Kwale-Kwale ya Kife a Jihar Neja Nijar ta ƙulla Yarjejeniyar Gina Matatar Mai da Kamfani a CanadaMabiya Addinai Biyu a Najeriya Sun Sanya Hannu Kan Sabuwar YarjejeniyaAn Kashe Matashi Kan Murfin Tayar Adaidaita Sahu a KanoMutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin Gargajiya
X whatsapp