Home Labarai Hukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗe

Hukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗe

Hukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗe

 

Babbar Kotun Jihar Akwa Ibom, ta yanke wa wani direban Keke Napep, Michael Effiong Japhet, hukuncin ɗaurin rai da rai bayan ta same shi da laifin aikata fyaɗe da kuma sata.

Mai shari’a Archibong Archibong, ya ce kotun ta gamsu da hujjojin da masu gabatar da ƙara suka bayar, inda ta tabbatar da cewa Japhet ya aikata laifukan da ake zargin sa da aikatawa.

Kotun ta yanke masa hukuncin ne bisa dokar laifukan fyaɗe ta Jihar Akwa Ibom ta shekarar 2000, bayan an same shi da laifin yi wa wata mata fyaɗe da kuma ƙwace mata kuɗi.

An bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar 23 ga watan Fabrairun 2015, lokacin da Japhet ya ɗauki wata mai sayar da kayan marmari daga Ekom Iman zuwa Iko Ofon a Ƙaramar Hukumar Ikono.

A maimakon kai ta inda ta nufa, an ce ya sauya hanya ya bi da ita zuwa wani waje da ba kowa, inda ya yi mata fyaɗe.

An kuma zarge shi da ƙwace jakarta mai ɗauke da kuɗin cinikinta na ranar Naira 7,000, duk da roƙon sa da ta yi kada ya cutar da ita.

Kotun ta ce bayan sauraron dukkanin shaidun, ta samu Japhet da laifin da ake tuhumarsa da shi, sannan ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai da rai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSS
X whatsapp