Home Labarai Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a Sokoto

Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a Sokoto

Sojoji

Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a Sokoto

 

Bayanai sun ce mayaƙan Lakurawa sun kai wa dakarun farmaki ne a yayin da suke ƙoƙarin gyara motar su da ta lalace a kan hanya.

Aƙalla sojojin Najeriya bakwai ne suka rasa rayukansu a wani harin kwanton ɓauna da ake zargin mayaƙa masu iƙirarin jihadi suka kai musu a Jihar Sakkwato Arewa maso Yamma.

Majiyoyin soji da na cikin gida sun bayyana cewa lamarin ya faru ne a daren Asabar, lokacin da dakarun ke dawowa daga wani samame da suka kan sansanin ’yan ƙungiyar Lakurawa a garin Illela da ke iyakar Najeriya da Jamhuriyyar Nijar.

Rahotanni sun ce mayaƙan sun kai wa sojojin hari ne bayan ɗaya daga ayarin motocinsu ta lalace a kan hanya, lamarin da ya tilasta mata tsayawa yayin da sauran motoci biyun suka ci gaba da tafiya.

Wata majiya ta shaida cewa mayaƙan Lakurawa sun kai wa dakarun farmaki ne a yayin da suke ƙoƙarin gyara motar, inda suka kashe sojoji bakwai ciki har da wani mai muƙamin Laftanar.

Wani mazaunin yankin ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa soja guda ɗaya ne ya tsira daga harin, yayin da sauran suka rasa rayukansu.

Rundunar Sojin Najeriya ta tabbatar da faruwar harin, sai dai ba ta bayyana adadin waɗanda suka mutu ba.

Kakakin rundunar, Laftanar Kanal Olaniyi Osoba, ya ce an tura ƙarin dakarun gaggawa zuwa yankin domin ci gaba da kai farmaki da kuma fatattakar maharan.

Ya ƙara da cewa ana ci gaba da gudanar da ayyukan tsaro domin gano tare da murƙushe waɗanda suka kai harin.

Ƙungiyar Lakurawa, wacce ake alaƙanta ta da wasu ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi a yankin Sahel, ta ƙara ƙarfi a jihohin Kebbi da Sakkwato tun daga 2018, inda ta fara zama barazanar tsaro musamman daga shekarar 2023.

A baya, rahotanni sun nuna cewa an sha gudanar da hare-haren haɗin gwiwa tsakanin Najeriya da ƙasashen waje kan sansanonin ƙungiyar a yankin.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp