Home Labarai Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a Sokoto

Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a Sokoto

Sojoji

Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a Sokoto

 

Bayanai sun ce mayaƙan Lakurawa sun kai wa dakarun farmaki ne a yayin da suke ƙoƙarin gyara motar su da ta lalace a kan hanya.

Aƙalla sojojin Najeriya bakwai ne suka rasa rayukansu a wani harin kwanton ɓauna da ake zargin mayaƙa masu iƙirarin jihadi suka kai musu a Jihar Sakkwato Arewa maso Yamma.

Majiyoyin soji da na cikin gida sun bayyana cewa lamarin ya faru ne a daren Asabar, lokacin da dakarun ke dawowa daga wani samame da suka kan sansanin ’yan ƙungiyar Lakurawa a garin Illela da ke iyakar Najeriya da Jamhuriyyar Nijar.

Rahotanni sun ce mayaƙan sun kai wa sojojin hari ne bayan ɗaya daga ayarin motocinsu ta lalace a kan hanya, lamarin da ya tilasta mata tsayawa yayin da sauran motoci biyun suka ci gaba da tafiya.

Wata majiya ta shaida cewa mayaƙan Lakurawa sun kai wa dakarun farmaki ne a yayin da suke ƙoƙarin gyara motar, inda suka kashe sojoji bakwai ciki har da wani mai muƙamin Laftanar.

Wani mazaunin yankin ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa soja guda ɗaya ne ya tsira daga harin, yayin da sauran suka rasa rayukansu.

Rundunar Sojin Najeriya ta tabbatar da faruwar harin, sai dai ba ta bayyana adadin waɗanda suka mutu ba.

Kakakin rundunar, Laftanar Kanal Olaniyi Osoba, ya ce an tura ƙarin dakarun gaggawa zuwa yankin domin ci gaba da kai farmaki da kuma fatattakar maharan.

Ya ƙara da cewa ana ci gaba da gudanar da ayyukan tsaro domin gano tare da murƙushe waɗanda suka kai harin.

Ƙungiyar Lakurawa, wacce ake alaƙanta ta da wasu ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi a yankin Sahel, ta ƙara ƙarfi a jihohin Kebbi da Sakkwato tun daga 2018, inda ta fara zama barazanar tsaro musamman daga shekarar 2023.

A baya, rahotanni sun nuna cewa an sha gudanar da hare-haren haɗin gwiwa tsakanin Najeriya da ƙasashen waje kan sansanonin ƙungiyar a yankin.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp