Home Labarai Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a Sokoto

Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a Sokoto

Sojoji

Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a Sokoto

 

Bayanai sun ce mayaƙan Lakurawa sun kai wa dakarun farmaki ne a yayin da suke ƙoƙarin gyara motar su da ta lalace a kan hanya.

Aƙalla sojojin Najeriya bakwai ne suka rasa rayukansu a wani harin kwanton ɓauna da ake zargin mayaƙa masu iƙirarin jihadi suka kai musu a Jihar Sakkwato Arewa maso Yamma.

Majiyoyin soji da na cikin gida sun bayyana cewa lamarin ya faru ne a daren Asabar, lokacin da dakarun ke dawowa daga wani samame da suka kan sansanin ’yan ƙungiyar Lakurawa a garin Illela da ke iyakar Najeriya da Jamhuriyyar Nijar.

Rahotanni sun ce mayaƙan sun kai wa sojojin hari ne bayan ɗaya daga ayarin motocinsu ta lalace a kan hanya, lamarin da ya tilasta mata tsayawa yayin da sauran motoci biyun suka ci gaba da tafiya.

Wata majiya ta shaida cewa mayaƙan Lakurawa sun kai wa dakarun farmaki ne a yayin da suke ƙoƙarin gyara motar, inda suka kashe sojoji bakwai ciki har da wani mai muƙamin Laftanar.

Wani mazaunin yankin ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa soja guda ɗaya ne ya tsira daga harin, yayin da sauran suka rasa rayukansu.

Rundunar Sojin Najeriya ta tabbatar da faruwar harin, sai dai ba ta bayyana adadin waɗanda suka mutu ba.

Kakakin rundunar, Laftanar Kanal Olaniyi Osoba, ya ce an tura ƙarin dakarun gaggawa zuwa yankin domin ci gaba da kai farmaki da kuma fatattakar maharan.

Ya ƙara da cewa ana ci gaba da gudanar da ayyukan tsaro domin gano tare da murƙushe waɗanda suka kai harin.

Ƙungiyar Lakurawa, wacce ake alaƙanta ta da wasu ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi a yankin Sahel, ta ƙara ƙarfi a jihohin Kebbi da Sakkwato tun daga 2018, inda ta fara zama barazanar tsaro musamman daga shekarar 2023.

A baya, rahotanni sun nuna cewa an sha gudanar da hare-haren haɗin gwiwa tsakanin Najeriya da ƙasashen waje kan sansanonin ƙungiyar a yankin.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp