Home Labarai HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko...

HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko Haram

HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko Haram

 

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan Adam ta Human Rights Watch (HRW) ta zargi hukumomin Najeriya da rashin adalci wajen gudanar da shari’o’in da suka shafi waɗanda ake zargi da zama ƴan ƙungiyar Boko Haram.

A wani rahoto da ta fitar ranar Laraba, ƙungiyar ta ce ba a yin adalci a shari’o’in da ake yi ga waɗanda rikicin Boko Haram ya shafa tsawon shekaru.

HRW ta ce shari’o’in sun fi mayar da hankali ne kan waɗanda ba su da wani matsayi mai girma a ƙungiyar, yayin da manyan waɗanda ake zargi da hannu wajen aikata manyan laifuka ke ci gaba da tsallake hukunci.

Ƙungiyar ta bayyana cewa akwai matsaloli masu yawa da suka shafi tsarin shari’ar ta’addanci da kuma rashin ingancin hujjojin da ake gabatarwa a kotu.

Ta ce wasu daga cikin shari’o’in sun dogara ne kawai kan amincewar waɗanda ake tuhuma da laifi, ba tare da shaidu ko cikakkun hujjoji da za su tabbatar da zargin ba.

HRW ta kuma ce wasu daga cikin waɗanda ake tuhumar ana zarginsu ne da taimaka wa ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai a yanayi da ka iya kasancewa an tilasta musu yin hakan.

Ƙungiyar ta kuma nuna shakku kan ingancin lauyoyin da kotu ke ware wa waɗanda ba su da ikon ɗaukar lauyoyi, inda ta ce hakan na iya hana su samun cikakkiyar kariya a shari’a.

Wannan suka na zuwa ne bayan da Najeriya ta ke ci gaba da shari’o’in ta’addanci a wannan shekara, inda sama da mutum 1,100 ake tuhuma da laifukan da suka shafi Boko Haram da ƙungiyar ISWAP.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta'addanciBinciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko HaramHukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar Yan SandaMutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'adda
X whatsapp