Home Labarai HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko...

HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko Haram

HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko Haram

 

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan Adam ta Human Rights Watch (HRW) ta zargi hukumomin Najeriya da rashin adalci wajen gudanar da shari’o’in da suka shafi waɗanda ake zargi da zama ƴan ƙungiyar Boko Haram.

A wani rahoto da ta fitar ranar Laraba, ƙungiyar ta ce ba a yin adalci a shari’o’in da ake yi ga waɗanda rikicin Boko Haram ya shafa tsawon shekaru.

HRW ta ce shari’o’in sun fi mayar da hankali ne kan waɗanda ba su da wani matsayi mai girma a ƙungiyar, yayin da manyan waɗanda ake zargi da hannu wajen aikata manyan laifuka ke ci gaba da tsallake hukunci.

Ƙungiyar ta bayyana cewa akwai matsaloli masu yawa da suka shafi tsarin shari’ar ta’addanci da kuma rashin ingancin hujjojin da ake gabatarwa a kotu.

Ta ce wasu daga cikin shari’o’in sun dogara ne kawai kan amincewar waɗanda ake tuhuma da laifi, ba tare da shaidu ko cikakkun hujjoji da za su tabbatar da zargin ba.

HRW ta kuma ce wasu daga cikin waɗanda ake tuhumar ana zarginsu ne da taimaka wa ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai a yanayi da ka iya kasancewa an tilasta musu yin hakan.

Ƙungiyar ta kuma nuna shakku kan ingancin lauyoyin da kotu ke ware wa waɗanda ba su da ikon ɗaukar lauyoyi, inda ta ce hakan na iya hana su samun cikakkiyar kariya a shari’a.

Wannan suka na zuwa ne bayan da Najeriya ta ke ci gaba da shari’o’in ta’addanci a wannan shekara, inda sama da mutum 1,100 ake tuhuma da laifukan da suka shafi Boko Haram da ƙungiyar ISWAP.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Rundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga PantamiGazawar Demarketing: Yadda Sukar Rarara Mai Cike da Kiyayya ga Pantami Ya Rushe Daga Yushau A. ShuaibƘungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin AikiDakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da su
X whatsapp