Home Labarai HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko...

HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko Haram

HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko Haram

 

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan Adam ta Human Rights Watch (HRW) ta zargi hukumomin Najeriya da rashin adalci wajen gudanar da shari’o’in da suka shafi waɗanda ake zargi da zama ƴan ƙungiyar Boko Haram.

A wani rahoto da ta fitar ranar Laraba, ƙungiyar ta ce ba a yin adalci a shari’o’in da ake yi ga waɗanda rikicin Boko Haram ya shafa tsawon shekaru.

HRW ta ce shari’o’in sun fi mayar da hankali ne kan waɗanda ba su da wani matsayi mai girma a ƙungiyar, yayin da manyan waɗanda ake zargi da hannu wajen aikata manyan laifuka ke ci gaba da tsallake hukunci.

Ƙungiyar ta bayyana cewa akwai matsaloli masu yawa da suka shafi tsarin shari’ar ta’addanci da kuma rashin ingancin hujjojin da ake gabatarwa a kotu.

Ta ce wasu daga cikin shari’o’in sun dogara ne kawai kan amincewar waɗanda ake tuhuma da laifi, ba tare da shaidu ko cikakkun hujjoji da za su tabbatar da zargin ba.

HRW ta kuma ce wasu daga cikin waɗanda ake tuhumar ana zarginsu ne da taimaka wa ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai a yanayi da ka iya kasancewa an tilasta musu yin hakan.

Ƙungiyar ta kuma nuna shakku kan ingancin lauyoyin da kotu ke ware wa waɗanda ba su da ikon ɗaukar lauyoyi, inda ta ce hakan na iya hana su samun cikakkiyar kariya a shari’a.

Wannan suka na zuwa ne bayan da Najeriya ta ke ci gaba da shari’o’in ta’addanci a wannan shekara, inda sama da mutum 1,100 ake tuhuma da laifukan da suka shafi Boko Haram da ƙungiyar ISWAP.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp