Home Taska Hukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar...

Hukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar Yan Sanda

Court

Hukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar Yan Sanda

 

Kotu a Ghana ta yanke wa wani matashi ɗan shekara 26 hukuncin ɗauri bayan kama shi da laifin yunƙurin satar motar ƴansanda.

Matashin mai suna Ebenezer Frimpong ya shiga motar sulke ta ƴansanda ya har ya fara tafiya bayan direban motar ya fita domin sayen magani a wani kemis, a watan Afrilun wannan shekarar.

Bireban motar, Joshua Denkyi ya ce matashin ya samu damar sace motar ne bayan ya tsaya sayen magani a lokacin da yake kan hanya.

An kama matashin ne bayan an bi shi da gudu yayin da yake ƙoƙarin tserewa da motar, inda daga baya ƴansanda suka tsare shi.

Alƙalin kotun ya buƙaci a yi wa matashin gwajin ƙwaƙwalwa domin tabbatar da cewa yana cikin hankalinsa.

Ebenezer ya amsa laifinsa, lamarin da ya sa alƙalin ya yanke masa hukuncin ɗaurin wata ɗaya a gidan yari.

Alƙalin ya ce ya yanke masa hukuncin wata ɗaya kacal ne saboda matashin ya amsa laifinsa kai tsaye ba tare da ɓata lokacin kotu ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta'addanciBinciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko HaramHukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar Yan SandaMutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'adda
X whatsapp