Home Taska Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar Adamawa

Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar Adamawa

Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar Adamawa

 

Mutum shida sun rasu, yayin da wasu huɗu suka jikkata bayan tsawa ta faɗa kansu a ƙauyen Dadiri-Tirgali da ke gundumar Garum a Ƙaramar Hukumar Ganye ta Jihar Adamawa.

Lamarin ya faru ne ranar Lahadi yayin da mamatan da waɗanda suka jikkata ke girbin gyaɗa ruwan sama kamar da bakin ƙwarya yana kwarara.

Shaidu sun ce huɗun da suka tsira suna karɓar magani a Babban Asibitin Ganye, yayin da al’ummar yankin suka shiga jimami sakamakon ibtila’in.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Ganye, Daniel Kamsobbi, da ya tabbatar da faruwar lamarin ya jajanta wa iyalan mamatan.

Ya ƙara da cewa an sallami wata uwa da ɗanta daga asibiti bayan an tabbatar da ƙoshin lafiyarsu, yayin da mutum biyu ke ci gaba da karɓar magani.

Ya ce an umarci ’yan sanda da sauran hukumomin tsaro su binciki musabbabin lamarin domin taimakawa wajen wayar da kan al’umma, musamman manoma da ke yawan aiki a gonaki lokacin damina.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp