Home Taska Matatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man...

Matatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man Fetur

Matatar Dangote

Matatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man Fetur

 

Masana sun yi gargaɗin cewa matakin na iya ƙara haifar da hauhawar farashin man fetur tare da rage darajar Naira.

Matatar Dangote ta sanar da cewa ta dakatar da amfani da Naira ta koma karɓar dalar Amurka wajen sayar da man fetur, dizal da kuma man jiragen sama.

Sabon tsarin wanda ya fara aiki nan take, zai shafi sayar da dukkan dangogin man fetur da ake ɗauka kai tsaye daga matatar da kuma waɗanda ake jigilar su ta ruwa.

Majiyoyi a masana’antar mai sun ce matakin ya biyo bayan yadda matatar ke sayen yawancin ɗanyen mai da dala, yayin da take sayar da man da ta tace a naira, lamarin da ya jefa ta cikin matsi na musayar kuɗi.

Wata majiya ta ce matatar na buƙatar fiye da jiragen ruwa 15 na ɗanyen mai a kowane wata, amma Kamfanin Man Fetur na Kasa NNPCL na iya samar da ƙasa da jirage uku kacal ne a ƙarƙashin yarjejeniyar sayen ɗanyen mai da naira.

Matakin kamfanin na Dangote da ke fitar da gangar mai 650,000 a kowacce rana ka iya haifar da hauhawan farashin man fetur tare kuma da rage darajar Naira wanda ka iya shafar masu karamin karfi.

Masana sun yi gargaɗin cewa matakin na iya ƙara haifar da hauhawar farashin man fetur tare da rage darajar Naira wanda hakan babu makawa zai shafi masu ƙaramin ƙarfi.

Masanin harkokin mai da iskar gas, Otunba Tunji Oyebanji, ya ce sauyin na nuna cewa yarjejeniyar sayen ɗanyen mai da naira ba ta gudana yadda aka tsara, saboda ƙarancin ɗanyen mai da ake samu da kuma yarjejeniyoyin da aka riga aka ƙulla na fitar da shi zuwa ƙasashen waje.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Matatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga Legas
X whatsapp