Home Taska Matatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man...

Matatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man Fetur

Matatar Dangote

Matatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man Fetur

 

Masana sun yi gargaɗin cewa matakin na iya ƙara haifar da hauhawar farashin man fetur tare da rage darajar Naira.

Matatar Dangote ta sanar da cewa ta dakatar da amfani da Naira ta koma karɓar dalar Amurka wajen sayar da man fetur, dizal da kuma man jiragen sama.

Sabon tsarin wanda ya fara aiki nan take, zai shafi sayar da dukkan dangogin man fetur da ake ɗauka kai tsaye daga matatar da kuma waɗanda ake jigilar su ta ruwa.

Majiyoyi a masana’antar mai sun ce matakin ya biyo bayan yadda matatar ke sayen yawancin ɗanyen mai da dala, yayin da take sayar da man da ta tace a naira, lamarin da ya jefa ta cikin matsi na musayar kuɗi.

Wata majiya ta ce matatar na buƙatar fiye da jiragen ruwa 15 na ɗanyen mai a kowane wata, amma Kamfanin Man Fetur na Kasa NNPCL na iya samar da ƙasa da jirage uku kacal ne a ƙarƙashin yarjejeniyar sayen ɗanyen mai da naira.

Matakin kamfanin na Dangote da ke fitar da gangar mai 650,000 a kowacce rana ka iya haifar da hauhawan farashin man fetur tare kuma da rage darajar Naira wanda ka iya shafar masu karamin karfi.

Masana sun yi gargaɗin cewa matakin na iya ƙara haifar da hauhawar farashin man fetur tare da rage darajar Naira wanda hakan babu makawa zai shafi masu ƙaramin ƙarfi.

Masanin harkokin mai da iskar gas, Otunba Tunji Oyebanji, ya ce sauyin na nuna cewa yarjejeniyar sayen ɗanyen mai da naira ba ta gudana yadda aka tsara, saboda ƙarancin ɗanyen mai da ake samu da kuma yarjejeniyoyin da aka riga aka ƙulla na fitar da shi zuwa ƙasashen waje.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga PantamiGazawar Demarketing: Yadda Sukar Rarara Mai Cike da Kiyayya ga Pantami Ya Rushe Daga Yushau A. ShuaibƘungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin AikiDakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da suƳan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari'a da ke Jihar KatsinaBa ma Goyon Bayan a Riƙa Tura Sojoji Domin Aikin Tsaro a Lokacin Zaɓe - INECJam'iyyar NDC ta Buƙaci Sanata Hanga da Gaya da su Sake Tunani Kan Sauya SheƙaYan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata MatarsaMutane 15 Sun Mutu a Sabon Harin Yan Bindiga a Jihar Benue Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi MataimakinsaJami'an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu a Jihar Sokoto 
X whatsapp