Home Taska Matatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man...

Matatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man Fetur

Matatar Dangote

Matatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man Fetur

 

Masana sun yi gargaɗin cewa matakin na iya ƙara haifar da hauhawar farashin man fetur tare da rage darajar Naira.

Matatar Dangote ta sanar da cewa ta dakatar da amfani da Naira ta koma karɓar dalar Amurka wajen sayar da man fetur, dizal da kuma man jiragen sama.

Sabon tsarin wanda ya fara aiki nan take, zai shafi sayar da dukkan dangogin man fetur da ake ɗauka kai tsaye daga matatar da kuma waɗanda ake jigilar su ta ruwa.

Majiyoyi a masana’antar mai sun ce matakin ya biyo bayan yadda matatar ke sayen yawancin ɗanyen mai da dala, yayin da take sayar da man da ta tace a naira, lamarin da ya jefa ta cikin matsi na musayar kuɗi.

Wata majiya ta ce matatar na buƙatar fiye da jiragen ruwa 15 na ɗanyen mai a kowane wata, amma Kamfanin Man Fetur na Kasa NNPCL na iya samar da ƙasa da jirage uku kacal ne a ƙarƙashin yarjejeniyar sayen ɗanyen mai da naira.

Matakin kamfanin na Dangote da ke fitar da gangar mai 650,000 a kowacce rana ka iya haifar da hauhawan farashin man fetur tare kuma da rage darajar Naira wanda ka iya shafar masu karamin karfi.

Masana sun yi gargaɗin cewa matakin na iya ƙara haifar da hauhawar farashin man fetur tare da rage darajar Naira wanda hakan babu makawa zai shafi masu ƙaramin ƙarfi.

Masanin harkokin mai da iskar gas, Otunba Tunji Oyebanji, ya ce sauyin na nuna cewa yarjejeniyar sayen ɗanyen mai da naira ba ta gudana yadda aka tsara, saboda ƙarancin ɗanyen mai da ake samu da kuma yarjejeniyoyin da aka riga aka ƙulla na fitar da shi zuwa ƙasashen waje.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dr Lawan Sani: Yadda Masanin Tsaron Intanet Ya Zama Sarkin Gumel: Daga Shuaib S. AgakaAllah ne Kawai Zai Iya Hana Tinubu Cin Nasara a 2027 — Datti"Dangantakar Farar Hula da Sojoji Itace Mabuɗi ga Tsaron Ƙasa da Shugabanci Nagari" — Tsohon CDS IraborRundunar Sojin Najeriya ta Binciki Zargin Cin Zarafin Jima'i da Aka yi wa Kyaftin a JosBabban Jami’in EFCC na Fuskantar Zarge-Zargen Cin Hanci da Dukiyar da ba a San Asalinta baƳan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan Gaba
X whatsapp