Home Taska Jami’an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu...

Jami’an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu a Jihar Sokoto 

Jami’an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu a Jihar Sokoto 

 

Rundunar ƴansandan jihar Sokoto ta sanar da cewa mutum huɗu sun mutu bayan da wasu ’yanbindiga suka kai hari a ƙauyen Maikujera da ke ƙaramar hukumar Rabah a jihar Sokoto.

Rundunar ta ce maharan sun kutsa yankin ne suna harbe-harbe tare da yin garkuwa da mutane da kuma satar dabbobi kafin jami’an tsaro su isa wurin.

A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce jami’anta tare da haɗin gwiwar dakarun soji sun bazama yankin bayan samun kiran gaggawa cewa ’yanbindiga suna wucewa da shanu da suka sace tare da mutane da suka yi garkuwa da su inda suka toshe hanyoyin da ake zargin ’yan bindigar za su bi wajen tserewa.

Hakan ya janyo musayar wuta mai tsanani tsakanin jami’an tsaro da maharan, lamarin da ya tilasta wa ’yan bindigar tserewa cikin daji tare da barin mutanen da suka yi garkuwa da su da kuma dabbobin da suka sace.

Rundunar ta ce ta samu nasarar kuɓutar da mutum 32 da aka yi garkuwa da su ba tare da sun ji rauni ba.

Waɗanda aka ceto sun haɗa da maza shida da mata 26, yawancinsu yara ne.

Kwamishinan ƴansandan jihar, Hayatu Hassan Shaffa, ya miƙa sakon ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka mutu tare da jaddada cewa jami’an tsaro na ci gaba da farautar ’yan bindigar domin gurfanar da su a gaban kuliya.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Yan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata MatarsaMutane 15 Sun Mutu a Sabon Harin Yan Bindiga a Jihar Benue Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi MataimakinsaJami'an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu a Jihar Sokoto China ba za ta Bayar ko ta Sayar wa Iran Makamai ba a Kowane h Hali - TrumpBai Dace Obasanjo ya Danganta Marigayi Ghali Na'abba da Zargin Cin Hanci ba - AtikuGarkuwa da Mutane: Dakarun Sojin Najeriya Sun Kama Mutane 5 a Jihar Yobe Sojojin Najeriya na Neman ɗaya Daga Cikin Jami'inta Ruwa a Jallo, Kan Zargin Sayar wa Ƴan bindiga Kakin SojiYaɗa Farfaganda da ƙiyayya Kan Gwamnati ba Zai Kawo ƙarshenta ba - MatawalleMawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar ShekaraShugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta'addanciBinciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko HaramHukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar Yan SandaMutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar Adamawa
X whatsapp