Home Taska Jami’an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu...

Jami’an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu a Jihar Sokoto 

Jami’an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu a Jihar Sokoto 

 

Rundunar ƴansandan jihar Sokoto ta sanar da cewa mutum huɗu sun mutu bayan da wasu ’yanbindiga suka kai hari a ƙauyen Maikujera da ke ƙaramar hukumar Rabah a jihar Sokoto.

Rundunar ta ce maharan sun kutsa yankin ne suna harbe-harbe tare da yin garkuwa da mutane da kuma satar dabbobi kafin jami’an tsaro su isa wurin.

A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce jami’anta tare da haɗin gwiwar dakarun soji sun bazama yankin bayan samun kiran gaggawa cewa ’yanbindiga suna wucewa da shanu da suka sace tare da mutane da suka yi garkuwa da su inda suka toshe hanyoyin da ake zargin ’yan bindigar za su bi wajen tserewa.

Hakan ya janyo musayar wuta mai tsanani tsakanin jami’an tsaro da maharan, lamarin da ya tilasta wa ’yan bindigar tserewa cikin daji tare da barin mutanen da suka yi garkuwa da su da kuma dabbobin da suka sace.

Rundunar ta ce ta samu nasarar kuɓutar da mutum 32 da aka yi garkuwa da su ba tare da sun ji rauni ba.

Waɗanda aka ceto sun haɗa da maza shida da mata 26, yawancinsu yara ne.

Kwamishinan ƴansandan jihar, Hayatu Hassan Shaffa, ya miƙa sakon ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka mutu tare da jaddada cewa jami’an tsaro na ci gaba da farautar ’yan bindigar domin gurfanar da su a gaban kuliya.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp