Home Taska China ba za ta Bayar ko ta Sayar wa Iran Makamai ba...

China ba za ta Bayar ko ta Sayar wa Iran Makamai ba a Kowane h Hali – Trump

Donald trump

China ba za ta Bayar ko ta Sayar wa Iran Makamai ba a Kowane 
Hali – Trump

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce shugabannin China da Rasha, Xi Jinping da Vladimir Putin, sun yi masa alƙawarin cewa ba za su sayar wa Iran makamai ba.

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, Trump ya ce Xi ya tabbatar masa a ganawarsu ta baya-bayan nan a Beijing cewa China ba za ta bayar ko ta sayar wa Iran makamai ba a kowane hali, har da kamfanonin ƙasar.

Trump ya ƙara da cewa shi ma Shugaban Rasha Vladimir Putin ya yi masa irin wannan alƙawari.

Ya ce Putin ya fahimci cewa Amurka ba ta sayar wa Ukraine makamai kai tsaye, sai dai ga ƙasashen ƙungiyar NATO, waɗanda ke biyan cikakken kuɗinsu.

“Kasashen biyu da aka fi dangantawa da Iran, ba na tsammanin suna da hannu. Kuma idan suna da hannu, hakan ba zai kasance cikin maslaharsu ba,” in ji Trump.

A baya-bayan nan kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito cewa hukumomin leƙen asirin Amurka na binciken yiwuwar Rasha ta taimaka wa Iran bayan hare-haren jirage marasa matuƙa da aka kai kan wasu cibiyoyin CIA a yankin Tekun Fasha.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
China ba za ta Bayar ko ta Sayar wa Iran Makamai ba a Kowane h Hali - TrumpBai Dace Obasanjo ya Danganta Marigayi Ghali Na'abba da Zargin Cin Hanci ba - AtikuGarkuwa da Mutane: Dakarun Sojin Najeriya Sun Kama Mutane 5 a Jihar Yobe Sojojin Najeriya na Neman ɗaya Daga Cikin Jami'inta Ruwa a Jallo, Kan Zargin Sayar wa Ƴan bindiga Kakin SojiYaɗa Farfaganda da ƙiyayya Kan Gwamnati ba Zai Kawo ƙarshenta ba - MatawalleMawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar ShekaraShugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta'addanciBinciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko HaramHukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar Yan SandaMutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗe
X whatsapp