Home Taska China ba za ta Bayar ko ta Sayar wa Iran Makamai ba...

China ba za ta Bayar ko ta Sayar wa Iran Makamai ba a Kowane h Hali – Trump

Donald trump

China ba za ta Bayar ko ta Sayar wa Iran Makamai ba a Kowane 
Hali – Trump

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce shugabannin China da Rasha, Xi Jinping da Vladimir Putin, sun yi masa alƙawarin cewa ba za su sayar wa Iran makamai ba.

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, Trump ya ce Xi ya tabbatar masa a ganawarsu ta baya-bayan nan a Beijing cewa China ba za ta bayar ko ta sayar wa Iran makamai ba a kowane hali, har da kamfanonin ƙasar.

Trump ya ƙara da cewa shi ma Shugaban Rasha Vladimir Putin ya yi masa irin wannan alƙawari.

Ya ce Putin ya fahimci cewa Amurka ba ta sayar wa Ukraine makamai kai tsaye, sai dai ga ƙasashen ƙungiyar NATO, waɗanda ke biyan cikakken kuɗinsu.

“Kasashen biyu da aka fi dangantawa da Iran, ba na tsammanin suna da hannu. Kuma idan suna da hannu, hakan ba zai kasance cikin maslaharsu ba,” in ji Trump.

A baya-bayan nan kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito cewa hukumomin leƙen asirin Amurka na binciken yiwuwar Rasha ta taimaka wa Iran bayan hare-haren jirage marasa matuƙa da aka kai kan wasu cibiyoyin CIA a yankin Tekun Fasha.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Ƴan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan GabaNDLEA Ta Kama Mai Safarar Hodar Iblis da ake Zargi da Laifi Akan Jigilar Kaya a Saudiyya, ta Kuma Kama Kwayoyi Masu Yaduwa Sama Da Miliyan 2Gwamnatin Tarayya ta Yaba da N5.41 Trillion da Kwastam ta Tara, Ta Nemi a bi Ka'idojin Duniya Hukumar Kwastam Ta Naɗa DCG, ACG 5, ta yi Nazarin Yadda aka Samu Kuɗin Shiga2027: HURIWA Ta Bukaci Ƴan Sanda da su Gurfanar da Ƴan Siyasa Kan Zargin Kalamai Masu Tada HankaliSojoji Sun Tarwatsa Maboyar Ƴan Ta'adda, Sun Kwace Bindigogin AK-47 a Sokoto 
X whatsapp