Home Taska China ba za ta Bayar ko ta Sayar wa Iran Makamai ba...

China ba za ta Bayar ko ta Sayar wa Iran Makamai ba a Kowane h Hali – Trump

Donald trump

China ba za ta Bayar ko ta Sayar wa Iran Makamai ba a Kowane 
Hali – Trump

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce shugabannin China da Rasha, Xi Jinping da Vladimir Putin, sun yi masa alƙawarin cewa ba za su sayar wa Iran makamai ba.

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, Trump ya ce Xi ya tabbatar masa a ganawarsu ta baya-bayan nan a Beijing cewa China ba za ta bayar ko ta sayar wa Iran makamai ba a kowane hali, har da kamfanonin ƙasar.

Trump ya ƙara da cewa shi ma Shugaban Rasha Vladimir Putin ya yi masa irin wannan alƙawari.

Ya ce Putin ya fahimci cewa Amurka ba ta sayar wa Ukraine makamai kai tsaye, sai dai ga ƙasashen ƙungiyar NATO, waɗanda ke biyan cikakken kuɗinsu.

“Kasashen biyu da aka fi dangantawa da Iran, ba na tsammanin suna da hannu. Kuma idan suna da hannu, hakan ba zai kasance cikin maslaharsu ba,” in ji Trump.

A baya-bayan nan kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito cewa hukumomin leƙen asirin Amurka na binciken yiwuwar Rasha ta taimaka wa Iran bayan hare-haren jirage marasa matuƙa da aka kai kan wasu cibiyoyin CIA a yankin Tekun Fasha.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp