Home SIYASA Bai Dace Obasanjo ya Danganta Marigayi Ghali Na’abba da Zargin Cin Hanci...

Bai Dace Obasanjo ya Danganta Marigayi Ghali Na’abba da Zargin Cin Hanci ba – Atiku

Bai Dace Obasanjo ya Danganta Marigayi Ghali Na’abba da Zargin Cin Hanci ba – Atiku

 

Tsohon Mataimakin Shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ya yi watsi da sabon zargin da tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo ya yi masa, yana mai cewa ƙoƙari ne na ɓata masa suna domin ba wa ɗan takarar da yake goyon baya gabanin zaɓen 2027.

A wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Phrank Shaibu ya fitar Atiku ya ce bai dace Obasanjo ya danganta marigayi tsohon Kakakin Majalisar Wakilai, Ghali Umar Na’Abba da zargin cin hanci ba, alhali ba ya raye don ya kare kansa.

Ya kuma ce, idan har akwai hujjar aikata laifin kamar yadda aka yi zargin ya kamata gwamnatin Obasanjo ta ɗauki mataki tun lokacin da lamarin ya faru.

Atiku ya yi zargin cewa, lokacin da aka sake tayar da batun na da alaƙa da shirye-shiryen siyasar zaben 2027, yana mai cewa tsohon shugaban ƙasar ya kamata ya fito fili ya bayyana ɗan takarar da yake goyon baya maimakon amfani da tsofaffin zarge-zarge wajen janyo ra’ayin jama’a.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp