Bai Dace Obasanjo ya Danganta Marigayi Ghali Na’abba da Zargin Cin Hanci ba – Atiku
Tsohon Mataimakin Shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ya yi watsi da sabon zargin da tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo ya yi masa, yana mai cewa ƙoƙari ne na ɓata masa suna domin ba wa ɗan takarar da yake goyon baya gabanin zaɓen 2027.
Read Also:
A wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Phrank Shaibu ya fitar Atiku ya ce bai dace Obasanjo ya danganta marigayi tsohon Kakakin Majalisar Wakilai, Ghali Umar Na’Abba da zargin cin hanci ba, alhali ba ya raye don ya kare kansa.
Ya kuma ce, idan har akwai hujjar aikata laifin kamar yadda aka yi zargin ya kamata gwamnatin Obasanjo ta ɗauki mataki tun lokacin da lamarin ya faru.
Atiku ya yi zargin cewa, lokacin da aka sake tayar da batun na da alaƙa da shirye-shiryen siyasar zaben 2027, yana mai cewa tsohon shugaban ƙasar ya kamata ya fito fili ya bayyana ɗan takarar da yake goyon baya maimakon amfani da tsofaffin zarge-zarge wajen janyo ra’ayin jama’a.












