Garkuwa da Mutane: Dakarun Sojin Najeriya Sun Kama Mutane 5 a Jihar Yobe
Dakarun Operation Hadin Kai na rundunar sojin Najeriya tare da haɗin gwiwar ƙungiyar maharba sun kama wasu mutane biyar da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a ƙauyen Jegalari da ke ƙaramar hukumar Fune a jihar Yobe.
Muƙaddashin jami’in yaɗa labarai na Operation Hadin Kai, Laftanar Mohammed Goni, ya ce an gudanar da wani samame a ranar Alhamis 23 ga watan Yulin 2026, bayan samun sahihan bayanan sirri kan ayyukan waɗanda ake zargin.
Read Also:
“Dakarun Bataliya ta 233 da ke sansanin soji na Damaturu ne suka gudanar da samamen bayan samun ingantattun bayanan sirri kan ayyukan waɗannan da ake zargin,” in ji nsanarwar da ya fitar
Ya ce dakarun sun ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda uku ƙirar gida, da bindiga pistol guda ɗaya da alburusai iri-iri da kuma wayoyi guda huɗu
Sanrwar ta ce a halin yanzu waɗanda ake zargin suna tsare a hannun sojoji tare da kayan da aka ƙwato domin ci gaba da bincike da kuma tantance rawar da suka taka a ayyukan garkuwa da mutane da sauran laifuka.
Rundunar ta ce za ta ci gaba da ƙaddamar da hare-haren domin hana ƴan ta’adda da sauran masu aikata laifuka samun damar gudanar da ayyukansu a yankin Arewa maso Gabas











