Home Taska Garkuwa da Mutane: Dakarun Sojin Najeriya Sun Kama Mutane 5 a Jihar...

Garkuwa da Mutane: Dakarun Sojin Najeriya Sun Kama Mutane 5 a Jihar Yobe 

Rundunar Soji

Garkuwa da Mutane: Dakarun Sojin Najeriya Sun Kama Mutane 5 a Jihar Yobe 

 

Dakarun Operation Hadin Kai na rundunar sojin Najeriya tare da haɗin gwiwar ƙungiyar maharba sun kama wasu mutane biyar da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a ƙauyen Jegalari da ke ƙaramar hukumar Fune a jihar Yobe.

Muƙaddashin jami’in yaɗa labarai na Operation Hadin Kai, Laftanar Mohammed Goni, ya ce an gudanar da wani samame a ranar Alhamis 23 ga watan Yulin 2026, bayan samun sahihan bayanan sirri kan ayyukan waɗanda ake zargin.

“Dakarun Bataliya ta 233 da ke sansanin soji na Damaturu ne suka gudanar da samamen bayan samun ingantattun bayanan sirri kan ayyukan waɗannan da ake zargin,” in ji nsanarwar da ya fitar

Ya ce dakarun sun ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda uku ƙirar gida, da bindiga pistol guda ɗaya da alburusai iri-iri da kuma wayoyi guda huɗu

Sanrwar ta ce a halin yanzu waɗanda ake zargin suna tsare a hannun sojoji tare da kayan da aka ƙwato domin ci gaba da bincike da kuma tantance rawar da suka taka a ayyukan garkuwa da mutane da sauran laifuka.

Rundunar ta ce za ta ci gaba da ƙaddamar da hare-haren domin hana ƴan ta’adda da sauran masu aikata laifuka samun damar gudanar da ayyukansu a yankin Arewa maso Gabas

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp