Home Taska Garkuwa da Mutane: Dakarun Sojin Najeriya Sun Kama Mutane 5 a Jihar...

Garkuwa da Mutane: Dakarun Sojin Najeriya Sun Kama Mutane 5 a Jihar Yobe 

Rundunar Soji

Garkuwa da Mutane: Dakarun Sojin Najeriya Sun Kama Mutane 5 a Jihar Yobe 

 

Dakarun Operation Hadin Kai na rundunar sojin Najeriya tare da haɗin gwiwar ƙungiyar maharba sun kama wasu mutane biyar da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a ƙauyen Jegalari da ke ƙaramar hukumar Fune a jihar Yobe.

Muƙaddashin jami’in yaɗa labarai na Operation Hadin Kai, Laftanar Mohammed Goni, ya ce an gudanar da wani samame a ranar Alhamis 23 ga watan Yulin 2026, bayan samun sahihan bayanan sirri kan ayyukan waɗanda ake zargin.

“Dakarun Bataliya ta 233 da ke sansanin soji na Damaturu ne suka gudanar da samamen bayan samun ingantattun bayanan sirri kan ayyukan waɗannan da ake zargin,” in ji nsanarwar da ya fitar

Ya ce dakarun sun ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda uku ƙirar gida, da bindiga pistol guda ɗaya da alburusai iri-iri da kuma wayoyi guda huɗu

Sanrwar ta ce a halin yanzu waɗanda ake zargin suna tsare a hannun sojoji tare da kayan da aka ƙwato domin ci gaba da bincike da kuma tantance rawar da suka taka a ayyukan garkuwa da mutane da sauran laifuka.

Rundunar ta ce za ta ci gaba da ƙaddamar da hare-haren domin hana ƴan ta’adda da sauran masu aikata laifuka samun damar gudanar da ayyukansu a yankin Arewa maso Gabas

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Ƴan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan GabaNDLEA Ta Kama Mai Safarar Hodar Iblis da ake Zargi da Laifi Akan Jigilar Kaya a Saudiyya, ta Kuma Kama Kwayoyi Masu Yaduwa Sama Da Miliyan 2Gwamnatin Tarayya ta Yaba da N5.41 Trillion da Kwastam ta Tara, Ta Nemi a bi Ka'idojin Duniya Hukumar Kwastam Ta Naɗa DCG, ACG 5, ta yi Nazarin Yadda aka Samu Kuɗin Shiga2027: HURIWA Ta Bukaci Ƴan Sanda da su Gurfanar da Ƴan Siyasa Kan Zargin Kalamai Masu Tada HankaliSojoji Sun Tarwatsa Maboyar Ƴan Ta'adda, Sun Kwace Bindigogin AK-47 a Sokoto 
X whatsapp