Home Taska Sojojin Najeriya na Neman ɗaya Daga Cikin Jami’inta Ruwa a Jallo, Kan...

Sojojin Najeriya na Neman ɗaya Daga Cikin Jami’inta Ruwa a Jallo, Kan Zargin Sayar wa Ƴan bindiga Kakin Soji

Sojojin Najeriya na Neman ɗaya Daga Cikin Jami’inta Ruwa a Jallo, Kan Zargin Sayar wa Ƴan bindiga Kakin Soji

 

 

Sashen kula da kayan aiki na rundunar sojin ƙasa ta Najeriya ta ayyana neman ɗaya daga cikin jami’inta ruwa a jallo, saboda zarginsa da sayar da kakin soji ga ”ƴanta’adda da masu aikata laifuka”.

Jami’in sojin wanda kurtu ne, mai suna Mohammed Yusuf Amutu tuni ya tsare daga wurin aikinsa bayan da zargin da ake yi masa ya fito fili.

Cikin wata sanarwar da sashen kula da kayan aikin soji na rundunar sojin ya fitar, ya ce yana ƙoƙarin gano inda sojan yake domin kama shi don fuskantar ladabtarwa.

Rundunar ta jaddada matsayin na rashin lamuntar saɓa wa aiki ko rashin ɗa’a ko duk wani abu da zai janyo wa rundunar sojin ƙasar barazana.

”Duk wani jami’inmu da muka samu da laifin taimaka wa ayyukan ƴanta’adda da masu aikata laifuka ko wasu ƙungiyoyi da gwamnati ta haramta, ta hanyar sayar musu da kakin soji ko wasu kayyaki, to zai fuskanci hukunci ƙarƙashin dokokin soji da kundin tsarin mulkin ƙasa”, kamar yadda sanarwar ta yi ƙarin haske.

Sanarwar ta kuma yi kira ga mutane su taimaka wajen kai rahoton jami’in a duk inda suka ganshi.

”Muna kira ga jama’a duk inda suka ganshi su yi ƙoƙarin sanar da sojoji mafi kusa da su ko wata hukumar tsaro mafi kusa”, in ji sanarwar.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp