Home SIYASA Yaɗa Farfaganda da ƙiyayya Kan Gwamnati ba Zai Kawo ƙarshenta ba –...

Yaɗa Farfaganda da ƙiyayya Kan Gwamnati ba Zai Kawo ƙarshenta ba – Matawalle

Yaɗa Farfaganda da ƙiyayya Kan Gwamnati ba Zai Kawo ƙarshenta ba – Matawalle

 

Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Mohammed Matawalle, ya buƙaci ƴan adawa da su daina yin abubuwan da ka iya tunzura ƴan Najeriya ko kuma ɓata sunan ƙasar a idon duniya.

A cikin wata sanarwa da kakakinsa Ahmad Dan-Wudil ya fitar, Matawalle ya ce abin takaici ne yadda ake zargin tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar ya ɗauki hayar kamfanonin kamun kafa na ƙasashen waje domin yaɗa tsofaffin takardu da suka shafi Shugaba Bola Tinubu a Amurka.

Ya ce hakan sam ba ya amfanar da dimokuraɗiyyar ƙasar.

“Maimakon ƙoƙarin ɓata sunan Najeriya da kuma ƙasƙantar da martabar ofishin shugaban ƙasa a ƙasashen waje, ya kamata ƴan adawa su mayar da hankali wajen tallafa wa ƙoƙarin gwamnati na magance matsalar tsaro, ƙarfafa haɗin kan ƙasa da kuma inganta rayuwar ƴan Najeriya,” in ji Ministan

Ya ce ofishin shugaban ƙasa na da martabarta, don haka ya kamata a mutunta shi duk da bambancin siyasa.

Matawalle ya kuma buga misali da yadda shugaban Amurka Donald Trump ya yaba wa Shugaba Tinubu kan jagorancinsa da kuma ƙoƙarin gwamnatinsa kan tsaro da yaƙi da ta’addanci.

Ministan ya ƙara da cewa yaɗa farfaganda da ƙiyayya kan gwamnati ba zai kawo ƙarshenta ba.

“Waɗanda suke tunanin cewa ƙarya da makirci za su kifar da gwamnatin Shugaba Tinubu suna yaudarar kansu, domin Najeriya ta ƴan Najeriya ce, kuma su ne za su sake yanke hukunci a zaɓen 2027,” in ji sanarwar

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Garkuwa da Mutane: Dakarun Sojin Najeriya Sun Kama Mutane 5 a Jihar Yobe Sojojin Najeriya na Neman ɗaya Daga Cikin Jami'inta Ruwa a Jallo, Kan Zargin Sayar wa Ƴan bindiga Kakin SojiYaɗa Farfaganda da ƙiyayya Kan Gwamnati ba Zai Kawo ƙarshenta ba - MatawalleMawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar ShekaraShugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta'addanciBinciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko HaramHukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar Yan SandaMutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar Tsaro
X whatsapp