Home SIYASA Yaɗa Farfaganda da ƙiyayya Kan Gwamnati ba Zai Kawo ƙarshenta ba –...

Yaɗa Farfaganda da ƙiyayya Kan Gwamnati ba Zai Kawo ƙarshenta ba – Matawalle

Yaɗa Farfaganda da ƙiyayya Kan Gwamnati ba Zai Kawo ƙarshenta ba – Matawalle

 

Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Mohammed Matawalle, ya buƙaci ƴan adawa da su daina yin abubuwan da ka iya tunzura ƴan Najeriya ko kuma ɓata sunan ƙasar a idon duniya.

A cikin wata sanarwa da kakakinsa Ahmad Dan-Wudil ya fitar, Matawalle ya ce abin takaici ne yadda ake zargin tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar ya ɗauki hayar kamfanonin kamun kafa na ƙasashen waje domin yaɗa tsofaffin takardu da suka shafi Shugaba Bola Tinubu a Amurka.

Ya ce hakan sam ba ya amfanar da dimokuraɗiyyar ƙasar.

“Maimakon ƙoƙarin ɓata sunan Najeriya da kuma ƙasƙantar da martabar ofishin shugaban ƙasa a ƙasashen waje, ya kamata ƴan adawa su mayar da hankali wajen tallafa wa ƙoƙarin gwamnati na magance matsalar tsaro, ƙarfafa haɗin kan ƙasa da kuma inganta rayuwar ƴan Najeriya,” in ji Ministan

Ya ce ofishin shugaban ƙasa na da martabarta, don haka ya kamata a mutunta shi duk da bambancin siyasa.

Matawalle ya kuma buga misali da yadda shugaban Amurka Donald Trump ya yaba wa Shugaba Tinubu kan jagorancinsa da kuma ƙoƙarin gwamnatinsa kan tsaro da yaƙi da ta’addanci.

Ministan ya ƙara da cewa yaɗa farfaganda da ƙiyayya kan gwamnati ba zai kawo ƙarshenta ba.

“Waɗanda suke tunanin cewa ƙarya da makirci za su kifar da gwamnatin Shugaba Tinubu suna yaudarar kansu, domin Najeriya ta ƴan Najeriya ce, kuma su ne za su sake yanke hukunci a zaɓen 2027,” in ji sanarwar

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp