Home SIYASA Yaɗa Farfaganda da ƙiyayya Kan Gwamnati ba Zai Kawo ƙarshenta ba –...

Yaɗa Farfaganda da ƙiyayya Kan Gwamnati ba Zai Kawo ƙarshenta ba – Matawalle

Yaɗa Farfaganda da ƙiyayya Kan Gwamnati ba Zai Kawo ƙarshenta ba – Matawalle

 

Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Mohammed Matawalle, ya buƙaci ƴan adawa da su daina yin abubuwan da ka iya tunzura ƴan Najeriya ko kuma ɓata sunan ƙasar a idon duniya.

A cikin wata sanarwa da kakakinsa Ahmad Dan-Wudil ya fitar, Matawalle ya ce abin takaici ne yadda ake zargin tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar ya ɗauki hayar kamfanonin kamun kafa na ƙasashen waje domin yaɗa tsofaffin takardu da suka shafi Shugaba Bola Tinubu a Amurka.

Ya ce hakan sam ba ya amfanar da dimokuraɗiyyar ƙasar.

“Maimakon ƙoƙarin ɓata sunan Najeriya da kuma ƙasƙantar da martabar ofishin shugaban ƙasa a ƙasashen waje, ya kamata ƴan adawa su mayar da hankali wajen tallafa wa ƙoƙarin gwamnati na magance matsalar tsaro, ƙarfafa haɗin kan ƙasa da kuma inganta rayuwar ƴan Najeriya,” in ji Ministan

Ya ce ofishin shugaban ƙasa na da martabarta, don haka ya kamata a mutunta shi duk da bambancin siyasa.

Matawalle ya kuma buga misali da yadda shugaban Amurka Donald Trump ya yaba wa Shugaba Tinubu kan jagorancinsa da kuma ƙoƙarin gwamnatinsa kan tsaro da yaƙi da ta’addanci.

Ministan ya ƙara da cewa yaɗa farfaganda da ƙiyayya kan gwamnati ba zai kawo ƙarshenta ba.

“Waɗanda suke tunanin cewa ƙarya da makirci za su kifar da gwamnatin Shugaba Tinubu suna yaudarar kansu, domin Najeriya ta ƴan Najeriya ce, kuma su ne za su sake yanke hukunci a zaɓen 2027,” in ji sanarwar

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Ƴan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan GabaNDLEA Ta Kama Mai Safarar Hodar Iblis da ake Zargi da Laifi Akan Jigilar Kaya a Saudiyya, ta Kuma Kama Kwayoyi Masu Yaduwa Sama Da Miliyan 2Gwamnatin Tarayya ta Yaba da N5.41 Trillion da Kwastam ta Tara, Ta Nemi a bi Ka'idojin Duniya Hukumar Kwastam Ta Naɗa DCG, ACG 5, ta yi Nazarin Yadda aka Samu Kuɗin Shiga2027: HURIWA Ta Bukaci Ƴan Sanda da su Gurfanar da Ƴan Siyasa Kan Zargin Kalamai Masu Tada HankaliSojoji Sun Tarwatsa Maboyar Ƴan Ta'adda, Sun Kwace Bindigogin AK-47 a Sokoto 
X whatsapp