Zaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasa
Jam’iyyar PDP tsagin Kabiru Turaki ta ce ta miƙa sunan tsohon shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan, ga Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) a matsayin ɗan takararta na shugaban ƙasa a zaɓen shekarar 2027.
Tsagin ya bayyana hakan ne ta bakin kakakin kwamitin riƙon ƙwarya na jam’iyyar, Ini Ememobong, a wani taron manema labarai da aka gudanar a Abuja.
Read Also:
A cewarsa, rikicin shugabanci da ya dabaibaye PDP bayan hukuncin Kotun Ƙoli ya haifar da kafa kwamitin riƙon ƙwarya domin tafiyar da harkokin jam’iyyar da kuma gudanar da muhimman ayyukanta.
Tsagin Turakin ya nace cewa shi ne halastaccen shugabancin PDP, wanda ya tsayar da Jonathan a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa tare da sauran ‘yan takarar gwamnoni, majalisun dokoki na tarayya da na jihohi.
Haka kuma ya ce ya ɗaukaka ƙara kan hukuncin da Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke kwanan nan dangane da rikicin shugabancin jam’iyyar.












