Home SIYASA Zaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan...

Zaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasa

Zaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasa

 

Jam’iyyar PDP tsagin Kabiru Turaki ta ce ta miƙa sunan tsohon shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan, ga Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) a matsayin ɗan takararta na shugaban ƙasa a zaɓen shekarar 2027.

Tsagin ya bayyana hakan ne ta bakin kakakin kwamitin riƙon ƙwarya na jam’iyyar, Ini Ememobong, a wani taron manema labarai da aka gudanar a Abuja.

A cewarsa, rikicin shugabanci da ya dabaibaye PDP bayan hukuncin Kotun Ƙoli ya haifar da kafa kwamitin riƙon ƙwarya domin tafiyar da harkokin jam’iyyar da kuma gudanar da muhimman ayyukanta.

Tsagin Turakin ya nace cewa shi ne halastaccen shugabancin PDP, wanda ya tsayar da Jonathan a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa tare da sauran ‘yan takarar gwamnoni, majalisun dokoki na tarayya da na jihohi.

Haka kuma ya ce ya ɗaukaka ƙara kan hukuncin da Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke kwanan nan dangane da rikicin shugabancin jam’iyyar.

 

 

 

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dr Lawan Sani: Yadda Masanin Tsaron Intanet Ya Zama Sarkin Gumel: Daga Shuaib S. AgakaAllah ne Kawai Zai Iya Hana Tinubu Cin Nasara a 2027 — Datti"Dangantakar Farar Hula da Sojoji Itace Mabuɗi ga Tsaron Ƙasa da Shugabanci Nagari" — Tsohon CDS IraborRundunar Sojin Najeriya ta Binciki Zargin Cin Zarafin Jima'i da Aka yi wa Kyaftin a JosBabban Jami’in EFCC na Fuskantar Zarge-Zargen Cin Hanci da Dukiyar da ba a San Asalinta baƳan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan Gaba
X whatsapp