Home SIYASA Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi Mataimakinsa

Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi Mataimakinsa

Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi Mataimakinsa

 

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya sanar da zaɓen mista Jerry Adams a matsayin mataimakinsa a zaɓen gwamnan 2027, bayan shawarwari da addu’o’i da ya ce sun jagoranci wannan mataki.

A cikin wata sanarwa da gwamnan ya fitar a shafinsa na X, Uba Sani ya ce zaɓar Adams ya yi daidai da manufar gwamnatinsa ta haɗin kai, adalci da bai wa kowane ɗan jihar damar jin yana da muhimmanci a harkokin gwamnati, ba tare da la’akari da addini ko ƙabila ba.

Ya bayyana cewa gwamnatinsa ta yi ƙoƙarin tabbatar da ci gaba a dukkan ƙananan hukumomin jihar tare da ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai tsakanin al’ummomi.

Gwamnan ya yaba wa Jerry Adams a matsayin gogaggen jami’in gwamnati kuma ƙwararren mai kula da harkokin haraji, yana mai cewa mutumin ne mai gaskiya, ƙwazo da kishin zaman lafiya, wanda zai taimaka wajen ci gaba da gina Kaduna mai haɗin kai da ci gaba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mabiya Addinai Biyu a Najeriya Sun Sanya Hannu Kan Sabuwar YarjejeniyaAn Kashe Matashi Kan Murfin Tayar Adaidaita Sahu a KanoMutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga Sojoji
X whatsapp