Home SIYASA Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi Mataimakinsa

Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi Mataimakinsa

Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi Mataimakinsa

 

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya sanar da zaɓen mista Jerry Adams a matsayin mataimakinsa a zaɓen gwamnan 2027, bayan shawarwari da addu’o’i da ya ce sun jagoranci wannan mataki.

A cikin wata sanarwa da gwamnan ya fitar a shafinsa na X, Uba Sani ya ce zaɓar Adams ya yi daidai da manufar gwamnatinsa ta haɗin kai, adalci da bai wa kowane ɗan jihar damar jin yana da muhimmanci a harkokin gwamnati, ba tare da la’akari da addini ko ƙabila ba.

Ya bayyana cewa gwamnatinsa ta yi ƙoƙarin tabbatar da ci gaba a dukkan ƙananan hukumomin jihar tare da ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai tsakanin al’ummomi.

Gwamnan ya yaba wa Jerry Adams a matsayin gogaggen jami’in gwamnati kuma ƙwararren mai kula da harkokin haraji, yana mai cewa mutumin ne mai gaskiya, ƙwazo da kishin zaman lafiya, wanda zai taimaka wajen ci gaba da gina Kaduna mai haɗin kai da ci gaba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp