Home SIYASA Babu Dan Takara ko Tikiti da zai iya Doke Namu a Zaɓen...

Babu Dan Takara ko Tikiti da zai iya Doke Namu a Zaɓen 2027 – Kwankwaso 

Babu Dan Takara ko Tikiti da zai iya Doke Namu a Zaɓen 2027 – Kwankwaso 

 

Jihar Kano – Dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar NDC, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana cewa tikitin da ya hada shi da Peter Obi ba shi da abokin hamayya wajen amincewar jama’a da kwarewa.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi 16 ga watan Agusta, 2026 a Abuja, inda ya ce hadin gwiwarsa da Obi zai iya kayar da duk wani dan takara a zaben shugaban kasa na 2027.

Jaridar Punch ta kuma ruwaito dan takarar yana mai cewa manufarsu ita ce samar da tikitin da zai hada ‘yan Najeriya ba tare da la’akari da yankinsu ko addininsu ba.

Kwankwaso ya bayyana karfinsu

Jaridar Daily Post ta wallafa cewa tsohon gwamnan Kano ya ce hadin kan nasu ya tattara goyon bayan Obi a Kudancin Najeriya da kuma tasirin siyasarsa a Arewa.

Ya kara da cewa wannan karfi da kowannensu ke da shi zai samar da babbar kafa ta siyasa da za ta hada al’ummar kasar baki daya.

Ya ce:

“Babu wani mutum ko tikiti da zai iya doke namu wajen amincewar jama’a, kwarewa da kuma, ba shakka, kaunar kasa.”

Kwankwaso ya kara da cewa tikitin nasu ya fi sauran ‘yan takara karfi idan aka yi la’akari da tausayin talakawan Najeriya da ke fama da matsaloli.

Ya ce:

“Ko ta fuskar tausaya wa talakawa da ke shan wahala a fadin kasar nan a yau, babu wani dan takara da zai iya yin gogayya da mu.”

Kwankwaso ya koda takararsa da Obi

Kwankwaso ya ce kwarewar da ya samu a zaben 2023 ta taimaka masa wajen fahimtar Obi sosai, lamarin da ya tabbatar masa cewa za su iya yin aiki tare.

A cewar Kwankwaso, Najeriya na bukatar sauyin siyasa saboda karuwar matsalar rashin tsaro, talauci, tabarbarewar ababen more rayuwa da kuma kalubalen da manoma ke fuskanta.

Ya ce cire tallafin man fetur bai kawo ingantuwar rayuwar ‘yan Najeriya ba, yayin da manoma ke ci gaba da fuskantar matsaloli saboda shigowar abinci daga kasashen waje cikin farashi mai sauki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Ƴan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan GabaNDLEA Ta Kama Mai Safarar Hodar Iblis da ake Zargi da Laifi Akan Jigilar Kaya a Saudiyya, ta Kuma Kama Kwayoyi Masu Yaduwa Sama Da Miliyan 2Gwamnatin Tarayya ta Yaba da N5.41 Trillion da Kwastam ta Tara, Ta Nemi a bi Ka'idojin Duniya Hukumar Kwastam Ta Naɗa DCG, ACG 5, ta yi Nazarin Yadda aka Samu Kuɗin Shiga2027: HURIWA Ta Bukaci Ƴan Sanda da su Gurfanar da Ƴan Siyasa Kan Zargin Kalamai Masu Tada HankaliSojoji Sun Tarwatsa Maboyar Ƴan Ta'adda, Sun Kwace Bindigogin AK-47 a Sokoto 
X whatsapp