Home SIYASA Babu Dan Takara ko Tikiti da zai iya Doke Namu a Zaɓen...

Babu Dan Takara ko Tikiti da zai iya Doke Namu a Zaɓen 2027 – Kwankwaso 

Babu Dan Takara ko Tikiti da zai iya Doke Namu a Zaɓen 2027 – Kwankwaso 

 

Jihar Kano – Dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar NDC, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana cewa tikitin da ya hada shi da Peter Obi ba shi da abokin hamayya wajen amincewar jama’a da kwarewa.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi 16 ga watan Agusta, 2026 a Abuja, inda ya ce hadin gwiwarsa da Obi zai iya kayar da duk wani dan takara a zaben shugaban kasa na 2027.

Jaridar Punch ta kuma ruwaito dan takarar yana mai cewa manufarsu ita ce samar da tikitin da zai hada ‘yan Najeriya ba tare da la’akari da yankinsu ko addininsu ba.

Kwankwaso ya bayyana karfinsu

Jaridar Daily Post ta wallafa cewa tsohon gwamnan Kano ya ce hadin kan nasu ya tattara goyon bayan Obi a Kudancin Najeriya da kuma tasirin siyasarsa a Arewa.

Ya kara da cewa wannan karfi da kowannensu ke da shi zai samar da babbar kafa ta siyasa da za ta hada al’ummar kasar baki daya.

Ya ce:

“Babu wani mutum ko tikiti da zai iya doke namu wajen amincewar jama’a, kwarewa da kuma, ba shakka, kaunar kasa.”

Kwankwaso ya kara da cewa tikitin nasu ya fi sauran ‘yan takara karfi idan aka yi la’akari da tausayin talakawan Najeriya da ke fama da matsaloli.

Ya ce:

“Ko ta fuskar tausaya wa talakawa da ke shan wahala a fadin kasar nan a yau, babu wani dan takara da zai iya yin gogayya da mu.”

Kwankwaso ya koda takararsa da Obi

Kwankwaso ya ce kwarewar da ya samu a zaben 2023 ta taimaka masa wajen fahimtar Obi sosai, lamarin da ya tabbatar masa cewa za su iya yin aiki tare.

A cewar Kwankwaso, Najeriya na bukatar sauyin siyasa saboda karuwar matsalar rashin tsaro, talauci, tabarbarewar ababen more rayuwa da kuma kalubalen da manoma ke fuskanta.

Ya ce cire tallafin man fetur bai kawo ingantuwar rayuwar ‘yan Najeriya ba, yayin da manoma ke ci gaba da fuskantar matsaloli saboda shigowar abinci daga kasashen waje cikin farashi mai sauki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp