Home Taska Ƙungiyar MURIC ta Zargi INEC da Hana Mata Masu Hijabi Kaɗa ƙuri’arsu...

Ƙungiyar MURIC ta Zargi INEC da Hana Mata Masu Hijabi Kaɗa ƙuri’arsu a Zaɓen Jihar Osun 

Ƙungiyar MURIC ta Zargi INEC da Hana Mata Masu Hijabi Kaɗa ƙuri’arsu a Zaɓen Jihar Osun 

Ƙungiyar Kare Haƙƙin Musulmi (MURIC) ta zargi Hukumar Zaɓe mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) da hana dubban mata Musulmi masu sanya hijabi kaɗa ƙuri’arsu a zaɓen gwamnan jihar Osun da aka gudanar ranar 15 ga Agusta, 2026.

A cikin wata sanarwa da daraktan ƙungiyar, Farfesa Ishaq Akintola, ya fitar, MURIC ta yi ikirarin cewa lamarin ya faru a wurare da dama na jihar, inda ta ce an hana wasu mata masu hijabi yin zaɓe sai bayan sun cire hijabinsu.

Kungiyar ta bayyana hakan a matsayin tauye haƙƙin zaɓe da kuma cin mutuncin mata Musulmi.

MURIC ta ɗora alhakin lamarin kan shugabancin INEC, tana mai cewa hukumar ta gaza wayar da kan jami’anta na dindindin da na wucin gadi game da ’yancin addini.

Kungiyar ta kuma ce tana da bidiyon wata mata mai hijabi da ta yi korafin cewa an hana ta yin zaɓe saboda suturar da take sanyawa.

Kungiyar ta sake kira da a cire shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan, tare da zargin cewa abin da ta kira tsoratar da mata Musulmi masu hijabi ya yi tasiri a sakamakon zaɓen.

Haka kuma MURIC ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta binciki zarge-zargen, tana mai gargadin cewa irin wannan matsala na iya sake faruwa a babban zaɓen shekarar 2027 idan ba a ɗauki mataki ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Ƴan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan GabaNDLEA Ta Kama Mai Safarar Hodar Iblis da ake Zargi da Laifi Akan Jigilar Kaya a Saudiyya, ta Kuma Kama Kwayoyi Masu Yaduwa Sama Da Miliyan 2Gwamnatin Tarayya ta Yaba da N5.41 Trillion da Kwastam ta Tara, Ta Nemi a bi Ka'idojin Duniya Hukumar Kwastam Ta Naɗa DCG, ACG 5, ta yi Nazarin Yadda aka Samu Kuɗin Shiga2027: HURIWA Ta Bukaci Ƴan Sanda da su Gurfanar da Ƴan Siyasa Kan Zargin Kalamai Masu Tada HankaliSojoji Sun Tarwatsa Maboyar Ƴan Ta'adda, Sun Kwace Bindigogin AK-47 a Sokoto 
X whatsapp