Home Taska Mutane 2 Sun Mutu Bayan Hatsarin Tankar Mai a Ibadan

Mutane 2 Sun Mutu Bayan Hatsarin Tankar Mai a Ibadan

Mutane 2 Sun Mutu Bayan Hatsarin Tankar Mai a Ibadan

Hukumar kashe gobara ta Jihar Oyo, ta tabbatar da mutuwar mutanen biyu, waɗanda suka maƙale a cikin tankar bayan aukuwar hatsarin.

Shugaban hukumar, Maroof Akinwande, ya ce hatsarin ya faru ne da safiyar ranar Asabar a kusa da gidan Guru Maharaji, a kan babbar hanyar Ibadan zuwa Legas.

cewarsa, bincike ya nuna cewa birkin tankar ne ya samu matsala yayin da direban ke tafiya, lamarin da ya sa motar ta kauce daga kan hanya tare da kifewa.

Jami’an kashe gobara sun isa wajen domin ceto mutanen da suka maƙale a cikin tankar.

Sai dai sun gano cewa mutane biyun sun riga sun rasu.

Daga bisani jami’an suka fitar da gawarwakinsu tare da miƙa su ga Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC).

Wani ganau, ya ce man fetur ne ya fara malala daga tankar zuwa kan babbar hanyar, lamarin da ya sa wasu mazauna yankin suka fito ɗauke da bokiti da jarkoki domin kwasar man.

Sai dai jami’an kashe gobara sun ɗauki matakin gaggawa tare da shawo kan lamarin kafin wuta ta tashi a wajen.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Ƴan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan GabaNDLEA Ta Kama Mai Safarar Hodar Iblis da ake Zargi da Laifi Akan Jigilar Kaya a Saudiyya, ta Kuma Kama Kwayoyi Masu Yaduwa Sama Da Miliyan 2Gwamnatin Tarayya ta Yaba da N5.41 Trillion da Kwastam ta Tara, Ta Nemi a bi Ka'idojin Duniya Hukumar Kwastam Ta Naɗa DCG, ACG 5, ta yi Nazarin Yadda aka Samu Kuɗin Shiga2027: HURIWA Ta Bukaci Ƴan Sanda da su Gurfanar da Ƴan Siyasa Kan Zargin Kalamai Masu Tada HankaliSojoji Sun Tarwatsa Maboyar Ƴan Ta'adda, Sun Kwace Bindigogin AK-47 a Sokoto 
X whatsapp