Home Taska Mutane 2 Sun Mutu Bayan Hatsarin Tankar Mai a Ibadan

Mutane 2 Sun Mutu Bayan Hatsarin Tankar Mai a Ibadan

Mutane 2 Sun Mutu Bayan Hatsarin Tankar Mai a Ibadan

Hukumar kashe gobara ta Jihar Oyo, ta tabbatar da mutuwar mutanen biyu, waɗanda suka maƙale a cikin tankar bayan aukuwar hatsarin.

Shugaban hukumar, Maroof Akinwande, ya ce hatsarin ya faru ne da safiyar ranar Asabar a kusa da gidan Guru Maharaji, a kan babbar hanyar Ibadan zuwa Legas.

cewarsa, bincike ya nuna cewa birkin tankar ne ya samu matsala yayin da direban ke tafiya, lamarin da ya sa motar ta kauce daga kan hanya tare da kifewa.

Jami’an kashe gobara sun isa wajen domin ceto mutanen da suka maƙale a cikin tankar.

Sai dai sun gano cewa mutane biyun sun riga sun rasu.

Daga bisani jami’an suka fitar da gawarwakinsu tare da miƙa su ga Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC).

Wani ganau, ya ce man fetur ne ya fara malala daga tankar zuwa kan babbar hanyar, lamarin da ya sa wasu mazauna yankin suka fito ɗauke da bokiti da jarkoki domin kwasar man.

Sai dai jami’an kashe gobara sun ɗauki matakin gaggawa tare da shawo kan lamarin kafin wuta ta tashi a wajen.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp