Home Taska Ƙungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

Ƙungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

Ƙungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

 

Ƙungiyar Likitoci Masu Neman Ƙwarewa a Najeriya (NARD) ta yi barazanar shiga yajin aiki na sai baba-ta-gani idan har gwamnatin tarayya ba ta biya buƙatunta ba.

NARD ta ce za ta tsunduma yajin aikin ne a ranar 10 ga watan Agusta saboda gaza biyan buƙatunta da suka shafi bashin albashi da inganta walwalarsu da kuma yanayin aiki ba.

Kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, ƙungiyar ta cimma wannan matsaya ne a ƙarshen taron Kwamitin zartarwarta da aka gudanar a Gombe daga ranar 26 zuwa 31 ga watan Yuli.

A yayin taron ne wakilan ƙungiyar suka duba yadda aka aiwatar da yarjejeniyoyin da aka cimma da gwamnatin tarayya a baya, tare da nazarin matsalolin da ke addabar fannin lafiya a ƙasar.

Shugaban NARD, Dakta Mohammad Usman Suleiman, ya ce ƙungiyar ta nuna rashin gamsuwa da yadda gwamnatin ke tafiyar hawainiya wajen cika alƙawuran da aka yi, duk da tattaunawa da aka shafe watanni ana yi.

Ya ce ƙungiyar ta tsawaita wa’adin yajin aikin har sau huɗu domin bai wa gwamnati damar warware matsalolin, amma ya ce har yanzu yawancin alƙawuran ba a cika su ba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Ƴan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan GabaNDLEA Ta Kama Mai Safarar Hodar Iblis da ake Zargi da Laifi Akan Jigilar Kaya a Saudiyya, ta Kuma Kama Kwayoyi Masu Yaduwa Sama Da Miliyan 2Gwamnatin Tarayya ta Yaba da N5.41 Trillion da Kwastam ta Tara, Ta Nemi a bi Ka'idojin Duniya Hukumar Kwastam Ta Naɗa DCG, ACG 5, ta yi Nazarin Yadda aka Samu Kuɗin Shiga2027: HURIWA Ta Bukaci Ƴan Sanda da su Gurfanar da Ƴan Siyasa Kan Zargin Kalamai Masu Tada HankaliSojoji Sun Tarwatsa Maboyar Ƴan Ta'adda, Sun Kwace Bindigogin AK-47 a Sokoto 
X whatsapp