Home Taska Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9...

Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da su

Rundunar Soji

Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da su

 

Jami’an tsaron Najeriya sun kashe wasu mutum uku da ake zargin ‘yan bindiga ne, tare da ceto mutum tara da aka yi garkuwa da su a wani samame da suka kai a jihar Kwara, kamar yadda shafin Channels Television mai zaman kansa ya ruwaito a ranar 30 ga Yuli.

An gudanar da samamen ne tare da haɗin gwiwar jami’an Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS), dakarun tsaron gandun daji da mafarauta da kuma ‘yan sa-kai a yankunan Obbo-Aiyegunle, Ejiu-Ora da Osi da ke ƙaramar hukumar Ekiti a jihar Kwara, kusa da iyakar jihar Neja.

An yi garkuwa da mutanen ne daga al’ummar Eju, kuma ana cikin tafiya da su ta cikin daji zuwa jihar Neja lokacin da jami’an tsaron suka kai dauki.

Jihar Kwara ta fuskanci ƙaruwa a hare-haren da ake kai wa fararen hula da jami’an tsaro cikin watannin baya-bayan nan.

A ranar 22 ga Yuli, Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya amince da kafa sabon bataliyar sojoji a jihar domin yaƙar masu aikata laifuka, ciki har da ‘yan bindiga da kuma ƙungiyar Mahmuda, wadda gwamnati ta bayyana a matsayin wani reshe na Boko Haram..

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mabiya Addinai Biyu a Najeriya Sun Sanya Hannu Kan Sabuwar YarjejeniyaAn Kashe Matashi Kan Murfin Tayar Adaidaita Sahu a KanoMutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga Sojoji
X whatsapp