Home Taska Ƴan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari’a da ke Jihar Katsina

Ƴan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari’a da ke Jihar Katsina

Ƴan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari’a da ke Jihar Katsina

 

Wasu ƴanbindiga sun kai hari a wata kotun shari’a da ke jihar Katsina a arewa maso yammacin Najeriya a ranar 29 ga Yuli, inda alƙalin kotun ya tsere kafin maharan su kutsa, kamar yadda Daily Trust mai zaman kanta ta ruwaito a ranar 30 ga Yuli.

Mazauna yankin sun ce Alƙali Mohammed Muktar ya tsere ta taga bayan ya hango maharan na tunkarar kotun da ke ƙauyen Gwarjo a ƙaramar hukumar Matazu.

Wani mazaunin yankin ya ce: “Ƴanbindigar sun shiga cikin kotun suna harbe-harben kan mai uwa da wabi, kuma suna ta tambayar inda alƙalin yake. Amma sai ya samu nasarar tserewa ta taga, sannan wani ɗan acaba ya taimaka masa kafin su iso.”

Wani ganau ya kuma ce maharan sun yi barazanar kashe Alƙali Muktar idan har ya sake dkomawa domin sauraron shari’o’i.

Mazauna yankin na ganin cewa ‘yan bindigar sun zo ne domin kashe alƙalin ko kuma su yi garkuwa da shi domin neman kuɗin fansa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mabiya Addinai Biyu a Najeriya Sun Sanya Hannu Kan Sabuwar YarjejeniyaAn Kashe Matashi Kan Murfin Tayar Adaidaita Sahu a KanoMutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga Sojoji
X whatsapp