Home Taska Ƴan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari’a da ke Jihar Katsina

Ƴan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari’a da ke Jihar Katsina

Ƴan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari’a da ke Jihar Katsina

 

Wasu ƴanbindiga sun kai hari a wata kotun shari’a da ke jihar Katsina a arewa maso yammacin Najeriya a ranar 29 ga Yuli, inda alƙalin kotun ya tsere kafin maharan su kutsa, kamar yadda Daily Trust mai zaman kanta ta ruwaito a ranar 30 ga Yuli.

Mazauna yankin sun ce Alƙali Mohammed Muktar ya tsere ta taga bayan ya hango maharan na tunkarar kotun da ke ƙauyen Gwarjo a ƙaramar hukumar Matazu.

Wani mazaunin yankin ya ce: “Ƴanbindigar sun shiga cikin kotun suna harbe-harben kan mai uwa da wabi, kuma suna ta tambayar inda alƙalin yake. Amma sai ya samu nasarar tserewa ta taga, sannan wani ɗan acaba ya taimaka masa kafin su iso.”

Wani ganau ya kuma ce maharan sun yi barazanar kashe Alƙali Muktar idan har ya sake dkomawa domin sauraron shari’o’i.

Mazauna yankin na ganin cewa ‘yan bindigar sun zo ne domin kashe alƙalin ko kuma su yi garkuwa da shi domin neman kuɗin fansa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp