Home Taska Ƴan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari’a da ke Jihar Katsina

Ƴan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari’a da ke Jihar Katsina

Ƴan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari’a da ke Jihar Katsina

 

Wasu ƴanbindiga sun kai hari a wata kotun shari’a da ke jihar Katsina a arewa maso yammacin Najeriya a ranar 29 ga Yuli, inda alƙalin kotun ya tsere kafin maharan su kutsa, kamar yadda Daily Trust mai zaman kanta ta ruwaito a ranar 30 ga Yuli.

Mazauna yankin sun ce Alƙali Mohammed Muktar ya tsere ta taga bayan ya hango maharan na tunkarar kotun da ke ƙauyen Gwarjo a ƙaramar hukumar Matazu.

Wani mazaunin yankin ya ce: “Ƴanbindigar sun shiga cikin kotun suna harbe-harben kan mai uwa da wabi, kuma suna ta tambayar inda alƙalin yake. Amma sai ya samu nasarar tserewa ta taga, sannan wani ɗan acaba ya taimaka masa kafin su iso.”

Wani ganau ya kuma ce maharan sun yi barazanar kashe Alƙali Muktar idan har ya sake dkomawa domin sauraron shari’o’i.

Mazauna yankin na ganin cewa ‘yan bindigar sun zo ne domin kashe alƙalin ko kuma su yi garkuwa da shi domin neman kuɗin fansa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Ƴan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan GabaNDLEA Ta Kama Mai Safarar Hodar Iblis da ake Zargi da Laifi Akan Jigilar Kaya a Saudiyya, ta Kuma Kama Kwayoyi Masu Yaduwa Sama Da Miliyan 2Gwamnatin Tarayya ta Yaba da N5.41 Trillion da Kwastam ta Tara, Ta Nemi a bi Ka'idojin Duniya Hukumar Kwastam Ta Naɗa DCG, ACG 5, ta yi Nazarin Yadda aka Samu Kuɗin Shiga2027: HURIWA Ta Bukaci Ƴan Sanda da su Gurfanar da Ƴan Siyasa Kan Zargin Kalamai Masu Tada HankaliSojoji Sun Tarwatsa Maboyar Ƴan Ta'adda, Sun Kwace Bindigogin AK-47 a Sokoto 
X whatsapp