Home Taska Ba ma Goyon Bayan a Riƙa Tura Sojoji Domin Aikin Tsaro a...

Ba ma Goyon Bayan a Riƙa Tura Sojoji Domin Aikin Tsaro a Lokacin Zaɓe – INEC

Amupitan

Ba ma Goyon Bayan a Riƙa Tura Sojoji Domin Aikin Tsaro a Lokacin Zaɓe – INEC

 

Hukumar zaɓe ta Najeriya, INEC ta ce ba ta goyon bayan a riƙa tura sojoji domin aikin tsaro a lokacin zaɓe

INEC ta ce ya kamata a riƙa amfani da sojoji ne kawai a lokutan da yanayin tsaro ya zama tilas ba wai a maida hakann al’ada ba.

Daily Trust ta ruwaito cewa shugaban hukumar, Farfesa Joash Amupitan, ne ya bayyana hakan ta bakin Daraktan Sashen Shari’a na INEC, Al-Hassan Umar, yayin da yake gabatar da jawabi a wani taron karawa juna sani da aka gudanar a Kwalejin Yaƙi ta Sojoji da ke Abuja.

Ya ce kundin tsarin mulkin Najeriya ya INEC ce ke da alhakin shiryawa, gudanarwa da kuma sa ido kan zaɓe.

Ya kuma ce rundunar ƴan sandan Najeriya ita ce hukuma ta farko da ke da alhakin tabbatar da tsaro a lokacin zaɓe

“Rawar da rundunar soji ke takawa ta musamman ce. Ana tura dakarun soji ne kawai idan halin tsaro ya yi muni domin su taimaka wa sauran hukumomi, kuma hakan yake a kundin tsarin mulki,” in ji shi

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp