Home Taska Yan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata Matarsa

Yan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata Matarsa

Yan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata Matarsa

 

Wasu ‘yan bindiga sun kashe wani Kanal mai aiki a rundunar sojin Najeriya, Abdussalam Ude, a wani hari da suka kai gidansa da ke yankin Kurudu a Abuja.

Majiyoyi sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da yammacin Litinin, jim kaɗan bayan Kanal Ude ya dawo gida daga wurin aikinsa.

Rahotanni sun ce maharan sun yi yunƙurin sace Kanal Ude ko kuma wasu daga cikin iyalansa kafin al’amura suka rikide zuwa harbe-harbe, cewar Vanguard.

A yayin harin, Kanal Ude ya mutu sakamakon harbin bindiga, yayin da matarsa, direbansa da jami’in tsaronsa suka samu raunuka.

An garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa asibiti domin samun kulawar likitoci, yayin da ake ci gaba da bibiyar lafiyarsu. Har yanzu ba a tabbatar da ainihin dalilin harin ba, kuma hukumomi ba su fitar da cikakken bayani kan abin da ya jawo lamarin ba.

Majiyoyin da ke da masaniya sun ce jami’an tsaro da hukumomin rundunar soji sun fara bincike domin gano waɗanda suka kai harin.

An ce Kanal Ude ɗan asalin Enugu ne, kuma ya yi aiki a sashen leƙen asirin rundunar sojin Najeriya tare da riƙe muƙamai masu muhimmanci.

Rahotanni sun nuna cewa ya halarci ayyukan yaƙi da masu tayar da ƙayar baya a Arewa maso Gabashin Najeriya, sannan ya yi aiki a ƙasashen Chadi da Faransa.

Abokan aikinsa sun bayyana shi a matsayin ƙwararren soja mai jajircewa da sadaukar da kai wajen gudanar da aikinsa cikin gaskiya da ƙwarewa.

Har zuwa lokacin da aka wallafa rahoton, rundunar sojin Najeriya ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance kan harin ba, yayin da ake sa ran ƙarin bayani bayan bincike.

Karin bayani na tafe….

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp