Yan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata Matarsa
Wasu ‘yan bindiga sun kashe wani Kanal mai aiki a rundunar sojin Najeriya, Abdussalam Ude, a wani hari da suka kai gidansa da ke yankin Kurudu a Abuja.
Majiyoyi sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da yammacin Litinin, jim kaɗan bayan Kanal Ude ya dawo gida daga wurin aikinsa.
Rahotanni sun ce maharan sun yi yunƙurin sace Kanal Ude ko kuma wasu daga cikin iyalansa kafin al’amura suka rikide zuwa harbe-harbe, cewar Vanguard.
A yayin harin, Kanal Ude ya mutu sakamakon harbin bindiga, yayin da matarsa, direbansa da jami’in tsaronsa suka samu raunuka.
Read Also:
An garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa asibiti domin samun kulawar likitoci, yayin da ake ci gaba da bibiyar lafiyarsu. Har yanzu ba a tabbatar da ainihin dalilin harin ba, kuma hukumomi ba su fitar da cikakken bayani kan abin da ya jawo lamarin ba.
Majiyoyin da ke da masaniya sun ce jami’an tsaro da hukumomin rundunar soji sun fara bincike domin gano waɗanda suka kai harin.
An ce Kanal Ude ɗan asalin Enugu ne, kuma ya yi aiki a sashen leƙen asirin rundunar sojin Najeriya tare da riƙe muƙamai masu muhimmanci.
Rahotanni sun nuna cewa ya halarci ayyukan yaƙi da masu tayar da ƙayar baya a Arewa maso Gabashin Najeriya, sannan ya yi aiki a ƙasashen Chadi da Faransa.
Abokan aikinsa sun bayyana shi a matsayin ƙwararren soja mai jajircewa da sadaukar da kai wajen gudanar da aikinsa cikin gaskiya da ƙwarewa.
Har zuwa lokacin da aka wallafa rahoton, rundunar sojin Najeriya ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance kan harin ba, yayin da ake sa ran ƙarin bayani bayan bincike.
Karin bayani na tafe….












