Home Taska Yan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata Matarsa

Yan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata Matarsa

Yan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata Matarsa

 

Wasu ‘yan bindiga sun kashe wani Kanal mai aiki a rundunar sojin Najeriya, Abdussalam Ude, a wani hari da suka kai gidansa da ke yankin Kurudu a Abuja.

Majiyoyi sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da yammacin Litinin, jim kaɗan bayan Kanal Ude ya dawo gida daga wurin aikinsa.

Rahotanni sun ce maharan sun yi yunƙurin sace Kanal Ude ko kuma wasu daga cikin iyalansa kafin al’amura suka rikide zuwa harbe-harbe, cewar Vanguard.

A yayin harin, Kanal Ude ya mutu sakamakon harbin bindiga, yayin da matarsa, direbansa da jami’in tsaronsa suka samu raunuka.

An garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa asibiti domin samun kulawar likitoci, yayin da ake ci gaba da bibiyar lafiyarsu. Har yanzu ba a tabbatar da ainihin dalilin harin ba, kuma hukumomi ba su fitar da cikakken bayani kan abin da ya jawo lamarin ba.

Majiyoyin da ke da masaniya sun ce jami’an tsaro da hukumomin rundunar soji sun fara bincike domin gano waɗanda suka kai harin.

An ce Kanal Ude ɗan asalin Enugu ne, kuma ya yi aiki a sashen leƙen asirin rundunar sojin Najeriya tare da riƙe muƙamai masu muhimmanci.

Rahotanni sun nuna cewa ya halarci ayyukan yaƙi da masu tayar da ƙayar baya a Arewa maso Gabashin Najeriya, sannan ya yi aiki a ƙasashen Chadi da Faransa.

Abokan aikinsa sun bayyana shi a matsayin ƙwararren soja mai jajircewa da sadaukar da kai wajen gudanar da aikinsa cikin gaskiya da ƙwarewa.

Har zuwa lokacin da aka wallafa rahoton, rundunar sojin Najeriya ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance kan harin ba, yayin da ake sa ran ƙarin bayani bayan bincike.

Karin bayani na tafe….

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mabiya Addinai Biyu a Najeriya Sun Sanya Hannu Kan Sabuwar YarjejeniyaAn Kashe Matashi Kan Murfin Tayar Adaidaita Sahu a KanoMutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga Sojoji
X whatsapp