Home SIYASA Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu 

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu 

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu 

 

Atiku ya ce kada ’yan ADC kada su karaya, “gwagwarmayar ceto Najeriya ba ta za ta ta’allaƙa kan hukuncin kotu guda ɗaya ba.

A jiya Litinin ce Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja ta tabbatar da hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ya haramta wa INEC amincewa ko halartar tarukan zaɓen shugabannin jihohin da kwamitin riƙon ƙwaryar ya shirya, tare da tabbatar da ci gaba da wa’adin shugabannin jihohin da aka zaɓa tun da farko.

Sai dai da take mayar da martani, ADC ta ce ta fara shirin ɗaukaka ƙarar, tana mai cewa ba ta yarda da hukuncin ba kuma tana ganin bai dace da doka ba.

Shi ma Atiku Abubakar, ta bakin mai ba shi shawara kan yaɗa labarai, Phrank Shuaibu, ya ce ya umarci lauyoyinsa su garzaya Kotun Ƙoli domin neman hukunci na ƙarshe kan lamarin.

Atiku ya ce saɓanin yadda wasu ke yaɗawa, hukuncin kotun bai soke zaɓen fidda gwani da jam’iyyar ADC ta gudanar domin tsayar da ’yan takararta a Zaɓen 2027 ba.

Ya ce “abin da wasu ke yaɗawa cewa hukuncin ya kawo ƙarshen takarar shugaban ƙasa ta ADC wani yunƙuri ne na yaɗa bayanan da ba su dace ba domin raunana ƴan adawa da kuma ruɗar da ’yan Najeriya.”

Atiku ya bayyana cewa hukuncin kotun ya shafi zaɓen shugabannin jam’iyyar a matakin ƙananan hukumomi ne da kuma wa’adin shugabannin kwamitocin riƙo na jihohi, ba zaɓen fidda gwani na tsayar da ’yan takara ba.

Ya kuma buƙaci magoya bayan ADC kada su karaya, inda ya ce “gwagwarmayar ceto Najeriya ba ta za ta ta’allaƙa kan hukuncin kotu guda ɗaya ba.”

 

 

 

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Meyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu MohammedJami'an Tsaro Sun Kai Farmaki Sansanin IPOB/ESN, Sun Kawar da 'Yan Ta'adda 6 a AnambraOperation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Lalata Motocin Yaƙi Guda Biyu na ISWAP, Sannan Ya Kawar da Ƴan Ta'adda da Dama a BornoMai fafutuka Mahdi Shehu ya yi Gargadin Cewa Kudirin Dokar NGO Zai iya Shafar Masallatai, Coci, da Ƙungiyoyin ɗalibaiRikicin Karkashin Mulkin APC a Katsina: ADC na Radda da CSO Har Yanzu Suna Tsare a Hannun Masu ba Tinubu Shawara, MasariAnambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron Hanya
X whatsapp