Home SIYASA Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu 

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu 

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu 

 

Atiku ya ce kada ’yan ADC kada su karaya, “gwagwarmayar ceto Najeriya ba ta za ta ta’allaƙa kan hukuncin kotu guda ɗaya ba.

A jiya Litinin ce Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja ta tabbatar da hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ya haramta wa INEC amincewa ko halartar tarukan zaɓen shugabannin jihohin da kwamitin riƙon ƙwaryar ya shirya, tare da tabbatar da ci gaba da wa’adin shugabannin jihohin da aka zaɓa tun da farko.

Sai dai da take mayar da martani, ADC ta ce ta fara shirin ɗaukaka ƙarar, tana mai cewa ba ta yarda da hukuncin ba kuma tana ganin bai dace da doka ba.

Shi ma Atiku Abubakar, ta bakin mai ba shi shawara kan yaɗa labarai, Phrank Shuaibu, ya ce ya umarci lauyoyinsa su garzaya Kotun Ƙoli domin neman hukunci na ƙarshe kan lamarin.

Atiku ya ce saɓanin yadda wasu ke yaɗawa, hukuncin kotun bai soke zaɓen fidda gwani da jam’iyyar ADC ta gudanar domin tsayar da ’yan takararta a Zaɓen 2027 ba.

Ya ce “abin da wasu ke yaɗawa cewa hukuncin ya kawo ƙarshen takarar shugaban ƙasa ta ADC wani yunƙuri ne na yaɗa bayanan da ba su dace ba domin raunana ƴan adawa da kuma ruɗar da ’yan Najeriya.”

Atiku ya bayyana cewa hukuncin kotun ya shafi zaɓen shugabannin jam’iyyar a matakin ƙananan hukumomi ne da kuma wa’adin shugabannin kwamitocin riƙo na jihohi, ba zaɓen fidda gwani na tsayar da ’yan takara ba.

Ya kuma buƙaci magoya bayan ADC kada su karaya, inda ya ce “gwagwarmayar ceto Najeriya ba ta za ta ta’allaƙa kan hukuncin kotu guda ɗaya ba.”

 

 

 

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga PantamiGazawar Demarketing: Yadda Sukar Rarara Mai Cike da Kiyayya ga Pantami Ya Rushe Daga Yushau A. ShuaibƘungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin AikiDakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da suƳan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari'a da ke Jihar KatsinaBa ma Goyon Bayan a Riƙa Tura Sojoji Domin Aikin Tsaro a Lokacin Zaɓe - INECJam'iyyar NDC ta Buƙaci Sanata Hanga da Gaya da su Sake Tunani Kan Sauya SheƙaYan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata MatarsaMutane 15 Sun Mutu a Sabon Harin Yan Bindiga a Jihar Benue Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi MataimakinsaJami'an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu a Jihar Sokoto 
X whatsapp