Home SIYASA Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba – Obi

Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba – Obi

Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba – Obi

 

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC a zaɓen 2027, Peter Obi, ya ce akwai yiwuwar ba zai iya kai lokacin babban zaɓe ba domin gwamnati tana yi masa bita-da-ƙulli.

Obi, ya bayyana hakan ne yayin wata hira da ya yi a shirin With Chude, wanda mai gabatar da shirye-shirye Chude Jideonwo ke jagoranta.

Tsohon gwamnan Jihar Anambra, ya ce irin matsin da yake fuskanta ya yi yawa har ba zai iya tabbatar da cewa zai kasance a raye domin fafatawa a zaɓen 2027 ba.

“Ba ma batun zama ɗan takara ba ne. Wataƙila ba zan kasance a raye ba. Ina faɗa muku wannan. Duk abin da nake yi domin na rayu, wannan gwamnati tana hana shi. Kuma da gangan take yi,” in ji Obi.

Sai dai Obi ya bayyana cewa yana zargin wani mutum kai-tsaye ba, amma ya ce abubuwan da yake fuskanta suna nuna akwai yunƙurin hana shi gudanar da ayyukansa.

“Ba zargi ba ne. Na sani. Ina fuskantar matsaloli a kullum. Ba za su zo kai-tsaye su ce, ‘muna yin wannan ba,’ amma za ka iya ganin hannunsu a kusan komai,” a cewarsa.

Obi, ya ce abin da yake faruwa ba shi kaɗai ya shafa ba, domin sauran ’yan adawa ma na fuskantar irin wannan matsin lamba.

“Suna matsa wa duk wanda yake adawa da su. Ana kai min hari kai tsaye. Komai,” in ji shi.

Ya kuma kawo misalin wani abin da ya ce ya faru a filin jirgin sama, inda ya zargi jami’ai da kulle masa mota yayin da suka bar sauran motoci.

“Kwanan nan na samu matsala a filin jirgin sama, inda wasu ma’aikata suka zo suka kulle min mota. Na ce musu, ‘Ni ne.’ Amma wanda ke kula da wsjen ya ce bai damu ba.”

Obi, ya ƙara da cewa wasu mutane suna guje wa nuna suna da alaƙa da shi a bainar jama’a saboda tsoron abin da ka iya faruwa da su.

“Ina ganin mutanen da na sani a filin jirgin sama, ba za su gaishe ni ba saboda suna tsoron abin da zai faru da su idan suka yi hakan.”

Ya kuma ce wasu magoya bayansa ma sun kan roƙe shi kada ya halarci wasu bukukuwan iyalansu domin gudun jawo musu matsala.

Har zuwa yanzu, Gwamnatin Tarayya ba ta mayar da martani kan zarge-zargen Peter Obi ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Ƴan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan GabaNDLEA Ta Kama Mai Safarar Hodar Iblis da ake Zargi da Laifi Akan Jigilar Kaya a Saudiyya, ta Kuma Kama Kwayoyi Masu Yaduwa Sama Da Miliyan 2Gwamnatin Tarayya ta Yaba da N5.41 Trillion da Kwastam ta Tara, Ta Nemi a bi Ka'idojin Duniya Hukumar Kwastam Ta Naɗa DCG, ACG 5, ta yi Nazarin Yadda aka Samu Kuɗin Shiga2027: HURIWA Ta Bukaci Ƴan Sanda da su Gurfanar da Ƴan Siyasa Kan Zargin Kalamai Masu Tada HankaliSojoji Sun Tarwatsa Maboyar Ƴan Ta'adda, Sun Kwace Bindigogin AK-47 a Sokoto 
X whatsapp