Home SIYASA Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba – Obi

Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba – Obi

Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba – Obi

 

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC a zaɓen 2027, Peter Obi, ya ce akwai yiwuwar ba zai iya kai lokacin babban zaɓe ba domin gwamnati tana yi masa bita-da-ƙulli.

Obi, ya bayyana hakan ne yayin wata hira da ya yi a shirin With Chude, wanda mai gabatar da shirye-shirye Chude Jideonwo ke jagoranta.

Tsohon gwamnan Jihar Anambra, ya ce irin matsin da yake fuskanta ya yi yawa har ba zai iya tabbatar da cewa zai kasance a raye domin fafatawa a zaɓen 2027 ba.

“Ba ma batun zama ɗan takara ba ne. Wataƙila ba zan kasance a raye ba. Ina faɗa muku wannan. Duk abin da nake yi domin na rayu, wannan gwamnati tana hana shi. Kuma da gangan take yi,” in ji Obi.

Sai dai Obi ya bayyana cewa yana zargin wani mutum kai-tsaye ba, amma ya ce abubuwan da yake fuskanta suna nuna akwai yunƙurin hana shi gudanar da ayyukansa.

“Ba zargi ba ne. Na sani. Ina fuskantar matsaloli a kullum. Ba za su zo kai-tsaye su ce, ‘muna yin wannan ba,’ amma za ka iya ganin hannunsu a kusan komai,” a cewarsa.

Obi, ya ce abin da yake faruwa ba shi kaɗai ya shafa ba, domin sauran ’yan adawa ma na fuskantar irin wannan matsin lamba.

“Suna matsa wa duk wanda yake adawa da su. Ana kai min hari kai tsaye. Komai,” in ji shi.

Ya kuma kawo misalin wani abin da ya ce ya faru a filin jirgin sama, inda ya zargi jami’ai da kulle masa mota yayin da suka bar sauran motoci.

“Kwanan nan na samu matsala a filin jirgin sama, inda wasu ma’aikata suka zo suka kulle min mota. Na ce musu, ‘Ni ne.’ Amma wanda ke kula da wsjen ya ce bai damu ba.”

Obi, ya ƙara da cewa wasu mutane suna guje wa nuna suna da alaƙa da shi a bainar jama’a saboda tsoron abin da ka iya faruwa da su.

“Ina ganin mutanen da na sani a filin jirgin sama, ba za su gaishe ni ba saboda suna tsoron abin da zai faru da su idan suka yi hakan.”

Ya kuma ce wasu magoya bayansa ma sun kan roƙe shi kada ya halarci wasu bukukuwan iyalansu domin gudun jawo musu matsala.

Har zuwa yanzu, Gwamnatin Tarayya ba ta mayar da martani kan zarge-zargen Peter Obi ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp