Home SIYASA Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba – Obi

Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba – Obi

Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba – Obi

 

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC a zaɓen 2027, Peter Obi, ya ce akwai yiwuwar ba zai iya kai lokacin babban zaɓe ba domin gwamnati tana yi masa bita-da-ƙulli.

Obi, ya bayyana hakan ne yayin wata hira da ya yi a shirin With Chude, wanda mai gabatar da shirye-shirye Chude Jideonwo ke jagoranta.

Tsohon gwamnan Jihar Anambra, ya ce irin matsin da yake fuskanta ya yi yawa har ba zai iya tabbatar da cewa zai kasance a raye domin fafatawa a zaɓen 2027 ba.

“Ba ma batun zama ɗan takara ba ne. Wataƙila ba zan kasance a raye ba. Ina faɗa muku wannan. Duk abin da nake yi domin na rayu, wannan gwamnati tana hana shi. Kuma da gangan take yi,” in ji Obi.

Sai dai Obi ya bayyana cewa yana zargin wani mutum kai-tsaye ba, amma ya ce abubuwan da yake fuskanta suna nuna akwai yunƙurin hana shi gudanar da ayyukansa.

“Ba zargi ba ne. Na sani. Ina fuskantar matsaloli a kullum. Ba za su zo kai-tsaye su ce, ‘muna yin wannan ba,’ amma za ka iya ganin hannunsu a kusan komai,” a cewarsa.

Obi, ya ce abin da yake faruwa ba shi kaɗai ya shafa ba, domin sauran ’yan adawa ma na fuskantar irin wannan matsin lamba.

“Suna matsa wa duk wanda yake adawa da su. Ana kai min hari kai tsaye. Komai,” in ji shi.

Ya kuma kawo misalin wani abin da ya ce ya faru a filin jirgin sama, inda ya zargi jami’ai da kulle masa mota yayin da suka bar sauran motoci.

“Kwanan nan na samu matsala a filin jirgin sama, inda wasu ma’aikata suka zo suka kulle min mota. Na ce musu, ‘Ni ne.’ Amma wanda ke kula da wsjen ya ce bai damu ba.”

Obi, ya ƙara da cewa wasu mutane suna guje wa nuna suna da alaƙa da shi a bainar jama’a saboda tsoron abin da ka iya faruwa da su.

“Ina ganin mutanen da na sani a filin jirgin sama, ba za su gaishe ni ba saboda suna tsoron abin da zai faru da su idan suka yi hakan.”

Ya kuma ce wasu magoya bayansa ma sun kan roƙe shi kada ya halarci wasu bukukuwan iyalansu domin gudun jawo musu matsala.

Har zuwa yanzu, Gwamnatin Tarayya ba ta mayar da martani kan zarge-zargen Peter Obi ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Zaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga PantamiGazawar Demarketing: Yadda Sukar Rarara Mai Cike da Kiyayya ga Pantami Ya Rushe Daga Yushau A. ShuaibƘungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin AikiDakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da suƳan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari'a da ke Jihar KatsinaBa ma Goyon Bayan a Riƙa Tura Sojoji Domin Aikin Tsaro a Lokacin Zaɓe - INECJam'iyyar NDC ta Buƙaci Sanata Hanga da Gaya da su Sake Tunani Kan Sauya SheƙaYan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata MatarsaMutane 15 Sun Mutu a Sabon Harin Yan Bindiga a Jihar Benue Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi MataimakinsaJami'an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu a Jihar Sokoto China ba za ta Bayar ko ta Sayar wa Iran Makamai ba a Kowane h Hali - Trump
X whatsapp