Home SIYASA Shugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka...

Shugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta’addanci

Shugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta’addanci

 

Shugaban Amurka Donald Trump ya yaba wa shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu kan abin da ya kira “ƙwazon jagorancinsa” wajen yaƙi da ta’addanci da kuma magance matsalar tsaro a Najeriya.

Fadar shugaban ƙasar ta ce, a cikin wata wasiƙa da Trump ya aike wa Tinubu, ya ce yana yaba wa shugaban Najeriyar kan ƙudurin da yake da shi na magance matsalolin da suka addabi ƙasar, musamman hare-haren da ke shafar al’ummomin Kiristoci.

Trump ya ce babban abin alfahari ne gare shi yana tare da Tinubu wajen yaƙi da ƴan ta’adda domin ƙarfafa Najeriya da bunƙasa ta.

Ya kuma bayyana cewa dangantakar Amurka da Najeriya na da matuƙar muhimmanci a wannan lokaci da rikice-rikice ke ƙaruwa a yammacin Afirka da sauran sassan duniya.

A cewarsa, ƙasashen biyu suna da buri ɗaya na yaƙi da ta’addanci ta kowane fanni, kuma yarjejeniyar haɗin gwiwar tsaro ta shekarar 2026 tsakanin Amurka da Najeriya ta samar da ingantaccen tsarin cimma wannan buri.

Trump ya ce yana alfahari da tura rundunar musamman ta sojojin Amurka domin horas da sojojin Najeriya tare da samar musu da ƙwarewa da kayan aiki da bayanan sirri da za su taimaka wajen kare ƙasar da kuma tabbatar da tsaron ‘yan ƙasa.

A cewar gwamnatin Najeriya ta hannun Bayo Onanuga, daga cikin nasarorin haɗin gwiwar da ƙasashen biyu suka ƙula akwai harin da aka kai ranar 16 ga Mayu kan maɓoyar mayaƙan ISIS a yankin Tafkin Chadi, wanda ta ce ya yi sanadin kashe babban jagoran ƙungiyar Abubakar Al-Minoki da wasu manyan kwamandojinsa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp