Home SIYASA Shugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka...

Shugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta’addanci

Shugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta’addanci

 

Shugaban Amurka Donald Trump ya yaba wa shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu kan abin da ya kira “ƙwazon jagorancinsa” wajen yaƙi da ta’addanci da kuma magance matsalar tsaro a Najeriya.

Fadar shugaban ƙasar ta ce, a cikin wata wasiƙa da Trump ya aike wa Tinubu, ya ce yana yaba wa shugaban Najeriyar kan ƙudurin da yake da shi na magance matsalolin da suka addabi ƙasar, musamman hare-haren da ke shafar al’ummomin Kiristoci.

Trump ya ce babban abin alfahari ne gare shi yana tare da Tinubu wajen yaƙi da ƴan ta’adda domin ƙarfafa Najeriya da bunƙasa ta.

Ya kuma bayyana cewa dangantakar Amurka da Najeriya na da matuƙar muhimmanci a wannan lokaci da rikice-rikice ke ƙaruwa a yammacin Afirka da sauran sassan duniya.

A cewarsa, ƙasashen biyu suna da buri ɗaya na yaƙi da ta’addanci ta kowane fanni, kuma yarjejeniyar haɗin gwiwar tsaro ta shekarar 2026 tsakanin Amurka da Najeriya ta samar da ingantaccen tsarin cimma wannan buri.

Trump ya ce yana alfahari da tura rundunar musamman ta sojojin Amurka domin horas da sojojin Najeriya tare da samar musu da ƙwarewa da kayan aiki da bayanan sirri da za su taimaka wajen kare ƙasar da kuma tabbatar da tsaron ‘yan ƙasa.

A cewar gwamnatin Najeriya ta hannun Bayo Onanuga, daga cikin nasarorin haɗin gwiwar da ƙasashen biyu suka ƙula akwai harin da aka kai ranar 16 ga Mayu kan maɓoyar mayaƙan ISIS a yankin Tafkin Chadi, wanda ta ce ya yi sanadin kashe babban jagoran ƙungiyar Abubakar Al-Minoki da wasu manyan kwamandojinsa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp