Home Taska Binciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa...

Binciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?

Binciken Gaskiya: Shin Gajimare ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?

 

 

A baya-bayan nan wani abin al’ajabi da ya ɓulla a kan babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna wanda ya ɗauki hankalin matafiya da ke bin hanyar.

Abin mai kama da gajimare ya riƙa ɓulɓulowa daga ƙarƙashin ƙasa, inda yake taruwa ya riƙa tashi sama yana bazuwa a gefe.

Tun a makon da ya gabata ne abun ya fara ɗaukar hankalin matafiya, waɗanda suke sauka daga ababen hawansu tare da shiga cikinsa domin ɗaukar hotuna.

Mutanen da dama dai kan ce gajimare ne ya faɗo a wurin, wani ala’amari da ba a saba gani ba.

Shin gajimaren ne?

Hukumar Kula da Ka’idojin Muhalli ta Najeriya, NESREA, ta ce ta fara bincike domin gano musabbabin ala’amarin.

A ranar Talata ne tawagar jami’an hukumar suka ziyarci wurin da ke kusa da garin Jere a jihar Kaduna domin gane wa idansu.

Cikin wata sanarwa da mataimakiyar daraktan yaɗa labarai na hukumar, Nwamaka Ejiofor, ta fitar, ta ce jami’an NESREA sun ziyarci wurin domin gudanar da bincike.

Ta kuma ce daga binciken farko da suka gudanar sun gano cewa kumfa ce ke taruwa a wurin ba gajimare ba kamar yadda wasu ke yaɗawa.

Binciken farko da hukumar NESREA ta yi ya nuna cewa wata babbar mota ce ɗauke da wasu sinadarai ta yi hatsari a kusa da wurin, wanda ya janyo zubewar sinadaran da take ɗauke da su.

Kodayake hukumar ba ta tabbatar da ainihin abin da ya haifar da tashin kumfar ba, amma ta ce tana kan bincike domin gano haƙiƙanin abin.

NESREA ta ce ta tattara bayanai daga jami’an gwamnati da mazauna yankin, sannan ta ɗauki samfurin kumfar da ƙasar wurin da kuma ruwan wani rafi da ke kusa domin faɗaɗa bincike.

Hukumar ta kuma gargaɗi jama’a su guji kusantar kumfar da ruwan da ke kusa da wurin da kuma ƙasar da ke kewaye da shi har sai an kammala binciken, domin kauce wa yiwuwar haɗuwa da wani abu mai illa ga lafiya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp