Home Taska Binciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa...

Binciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?

Binciken Gaskiya: Shin Gajimare ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?

 

 

A baya-bayan nan wani abin al’ajabi da ya ɓulla a kan babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna wanda ya ɗauki hankalin matafiya da ke bin hanyar.

Abin mai kama da gajimare ya riƙa ɓulɓulowa daga ƙarƙashin ƙasa, inda yake taruwa ya riƙa tashi sama yana bazuwa a gefe.

Tun a makon da ya gabata ne abun ya fara ɗaukar hankalin matafiya, waɗanda suke sauka daga ababen hawansu tare da shiga cikinsa domin ɗaukar hotuna.

Mutanen da dama dai kan ce gajimare ne ya faɗo a wurin, wani ala’amari da ba a saba gani ba.

Shin gajimaren ne?

Hukumar Kula da Ka’idojin Muhalli ta Najeriya, NESREA, ta ce ta fara bincike domin gano musabbabin ala’amarin.

A ranar Talata ne tawagar jami’an hukumar suka ziyarci wurin da ke kusa da garin Jere a jihar Kaduna domin gane wa idansu.

Cikin wata sanarwa da mataimakiyar daraktan yaɗa labarai na hukumar, Nwamaka Ejiofor, ta fitar, ta ce jami’an NESREA sun ziyarci wurin domin gudanar da bincike.

Ta kuma ce daga binciken farko da suka gudanar sun gano cewa kumfa ce ke taruwa a wurin ba gajimare ba kamar yadda wasu ke yaɗawa.

Binciken farko da hukumar NESREA ta yi ya nuna cewa wata babbar mota ce ɗauke da wasu sinadarai ta yi hatsari a kusa da wurin, wanda ya janyo zubewar sinadaran da take ɗauke da su.

Kodayake hukumar ba ta tabbatar da ainihin abin da ya haifar da tashin kumfar ba, amma ta ce tana kan bincike domin gano haƙiƙanin abin.

NESREA ta ce ta tattara bayanai daga jami’an gwamnati da mazauna yankin, sannan ta ɗauki samfurin kumfar da ƙasar wurin da kuma ruwan wani rafi da ke kusa domin faɗaɗa bincike.

Hukumar ta kuma gargaɗi jama’a su guji kusantar kumfar da ruwan da ke kusa da wurin da kuma ƙasar da ke kewaye da shi har sai an kammala binciken, domin kauce wa yiwuwar haɗuwa da wani abu mai illa ga lafiya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp