Home SIYASA Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne – PDP

Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne – PDP

Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne – PDP

 

Jam’iyyar PDP tsagin Tanimu Turaki ta nuna damuwa kan hukuncin da Babbar Kotun Tarayya da ke Lokoja ta yanke kan soke rijistar jam’iyyar NDC, inda ta ce hakan koma baya ga dimokuraɗiyya a Najeriya.

A cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran jam’iyyar na riƙo, Ini Ememobong, ya fitar, PDP ta ce ko da yake tana jiran samun cikakken bayani dangane da hukuncin kotun, ta yi alawadai da abin da ta kira “murƙushe dimokuraɗiyya” a ƙasar.

Jam’iyyar ta ce hukuncin ya zo ne bayan ƴan Najeriya da dama sun kashe kuɗaɗe domin neman muƙaman siyasa a ƙarƙashin NDC.

“Wannan hukunci ba wai yana takaita tsarin jam’iyyu ba ne kawai, yana haifar da asara ga ƴan Najeriya da suka sa rai a jam’iyyar,” in ji sanarwar.

PDP ta kuma zargi gwamnatin ƙasar ƙarƙashin jam’iyyar APC da ƙoƙarin dakushe jam’iyyun adawa gabanin babban zaɓen shekarar 2027, domin bai wa Tinubu damar sake tsayawa takara ba tare da wani ƙalubale.

Jam’iyyar ta buƙaci shugabannin NDC su ƙalubalanci hukuncin a kotun ɗaukaka ƙara, tare da kira ga gwamnatin tarayya da ta daina abin da take yi domin zaman lafiya da kuma tabbatar da dorewar dimokuraɗiyya a ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp