Home SIYASA Obi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na...

Obi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam’iyyar NDC 

Obi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam’iyyar NDC 

 

Ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar NDC, Peter Obi ya zargi Gwamnatin Tarayya da ƙulla maƙarƙashiyar hana shi yin takara a zaɓen shekarar 2027.

Yayin da yake jawabi a wani shirin horas da shugabanci da Ƙungiyar ‘NextGen Mentorship and Leadership Initiative‘ ta shirya a Jami’ar Madonna da ke Okija a Jihar Anambra ranar Juma’a, Obi ya yi iƙirarin cewa ana yin iƙirarin dakatar da shi daga shiga zaɓe mai zuwa.

“Idan na gaya muku abubuwan da nake fuskanta a yau, ba za ku ganni a nan ba. Mutane sun tambaye ni, ‘Shin har yanzu za ka je Madonna?’ Sai na ce, ‘Eh. Zan je.’ Suka ce da duk abubuwan da ke faruwa a Najeriya, har yanzu za ka je can, sai na ce, ‘Eh. Na ga mafi muninsa.’ A yau, Gwamnatin Tarayyar Najeriya tana yin duk mai yiwuwa don tabbatar da cewa ban zama ɗan takara a wannan zaɓen ba, amma ina gaya muku cewa ba za su yi nasara ba.”

“Idan kana rayuwa a inda babu ƙalubale, to ba ka rayuwa ne. Kada ku kalli ƙalubale, ƙalubale za su kasance a koyaushe. Ni ba ƙalubale nake kallo ba, burina shi ne inda na dosa. Na fi mayar da hankali ne kan sakamako mai kyau na inda na dosa, kuma hakan shi ne abin da yake ba ni ƙwarin gwiwa,” in ji shi.

Haka kuma Obi ya ƙalubalanci dukkan masu neman takarar shugaban ƙasa, ciki har da Shugaba Bola Tinubu, da su fito muhawarar bainar jama’a kan tsare-tsaren da suke da shi ga ƙasar.

“Ina ƙalubalantar duk wani mai takara da ya fito mu yi muhawara don ya faɗi abin da yake son yi wa wannan ƙasa, ciki har da Shugaba Bola Tinubu. Ba don na faranta muku rai nake faɗin hakan ba, a’a, don a canza Najeriya kuma a gyara ta,” in ji shi.

Tsohon Gwamnan na Jihar Anambra ya shaida wa ɗaliban cewa ba burin kansa ba ne yake yi, a’a, don muradin ganin ƙasar ta gyaru ne.

Haka kuma Obi ya yi tsokaci game da hukuncin Babbar Kotun Tarayya wadda ta soke wani hukunci na baya da ke umartar Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) da ta yi rajistar Jam’iyyar NDC a matsayin jam’iyyar siyasa.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa wata Babbar Kotun Tarayya da ke Lokoja ta soke hukuncinta na baya wanda ya umarci INEC da ta yi rajistar NDC a matsayin jam’iyyar siyasa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp