Home SIYASA Obi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na...

Obi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam’iyyar NDC 

Obi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam’iyyar NDC 

 

Ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar NDC, Peter Obi ya zargi Gwamnatin Tarayya da ƙulla maƙarƙashiyar hana shi yin takara a zaɓen shekarar 2027.

Yayin da yake jawabi a wani shirin horas da shugabanci da Ƙungiyar ‘NextGen Mentorship and Leadership Initiative‘ ta shirya a Jami’ar Madonna da ke Okija a Jihar Anambra ranar Juma’a, Obi ya yi iƙirarin cewa ana yin iƙirarin dakatar da shi daga shiga zaɓe mai zuwa.

“Idan na gaya muku abubuwan da nake fuskanta a yau, ba za ku ganni a nan ba. Mutane sun tambaye ni, ‘Shin har yanzu za ka je Madonna?’ Sai na ce, ‘Eh. Zan je.’ Suka ce da duk abubuwan da ke faruwa a Najeriya, har yanzu za ka je can, sai na ce, ‘Eh. Na ga mafi muninsa.’ A yau, Gwamnatin Tarayyar Najeriya tana yin duk mai yiwuwa don tabbatar da cewa ban zama ɗan takara a wannan zaɓen ba, amma ina gaya muku cewa ba za su yi nasara ba.”

“Idan kana rayuwa a inda babu ƙalubale, to ba ka rayuwa ne. Kada ku kalli ƙalubale, ƙalubale za su kasance a koyaushe. Ni ba ƙalubale nake kallo ba, burina shi ne inda na dosa. Na fi mayar da hankali ne kan sakamako mai kyau na inda na dosa, kuma hakan shi ne abin da yake ba ni ƙwarin gwiwa,” in ji shi.

Haka kuma Obi ya ƙalubalanci dukkan masu neman takarar shugaban ƙasa, ciki har da Shugaba Bola Tinubu, da su fito muhawarar bainar jama’a kan tsare-tsaren da suke da shi ga ƙasar.

“Ina ƙalubalantar duk wani mai takara da ya fito mu yi muhawara don ya faɗi abin da yake son yi wa wannan ƙasa, ciki har da Shugaba Bola Tinubu. Ba don na faranta muku rai nake faɗin hakan ba, a’a, don a canza Najeriya kuma a gyara ta,” in ji shi.

Tsohon Gwamnan na Jihar Anambra ya shaida wa ɗaliban cewa ba burin kansa ba ne yake yi, a’a, don muradin ganin ƙasar ta gyaru ne.

Haka kuma Obi ya yi tsokaci game da hukuncin Babbar Kotun Tarayya wadda ta soke wani hukunci na baya da ke umartar Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) da ta yi rajistar Jam’iyyar NDC a matsayin jam’iyyar siyasa.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa wata Babbar Kotun Tarayya da ke Lokoja ta soke hukuncinta na baya wanda ya umarci INEC da ta yi rajistar NDC a matsayin jam’iyyar siyasa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp