Home SIYASA Abinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu – Gwamnan Ahmed Aliyu 

Abinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu – Gwamnan Ahmed Aliyu 

Abinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu – Gwamnan Ahmed Aliyu 

 

Gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, ya ce shaye-shayen miyagun ƙwayoyi ne ke haddasa kusan kashi 80 na matsalolin tsaro da jihar ke fuskanta.

Aliyu ya ce mafi yawan masu aikata laifuka a jihar da ƴanbindiga na amfani da miyagun ƙwayoyi kafin su aikata ta’addanci.

Gwamnan wanda mataimakinsa, Idris Mohammed Gobir, ya wakilta ya bayyana hakan ne a yayin wani taron lacca da aka shirya domin tunawa da ranar yaƙi da shan miyagun ƙwayoyi da safararsu.

“Kashi 80 cikin 100 na matsalolin tsaron da ke addabar jiharmu suna da alaƙa da shan miyagun ƙwayoyi. Waɗannan mutane na amfani da ƙwayoyi masu haɗari. Mutumin da yake cikin hankalinsa ba zai dubi wani ɗan adam ya kashe shi ba,” in ji shi.

Aliyu ya kuma buƙaci matasa su guji shiga harkar shaye-shaye da safarar miyagun ƙwayoyi domin samun damar zama shugabanni da fitattun mutane a nan gaba.

Ya ce gwamnatin jihar ta kafa ofishin babban mataimaki na musamman kan daƙile shaye-shayen miyagun ƙwayoyi domin jagorantar shirye-shiryen wayar da kan jama’a.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Abinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban JosMatsalar Tsaro:  An Kashe Manoma 6 a Jihar Kaduna An Zargi Kwankwaso da Sayen Fom ɗin Takara na Kujeru 69 a Jam'iyyar PRPƘasurgumin ɗan bindiga, Turji ya ɗauki Alhakin Kashe Sojoji a Jihar SokotoMasu Iƙirarin Jihadi Sun Hallaka Manoma 11 a Jihar Borno 'Yan Bindiga sun ƙone shingen Jami'an NSCDC Tare da Garkuwa da Mutum 1 a Jihar KebbiTaron NUJ: Lokacin Da Manyan Jami’an Tsaro Suka Guji Yan Jarida Daga Yushau A. ShuaibSamar da Tsaro: Sojojin Najeriya sun Kama ƴan ƙasashen Wajen 46Ta'addanci: Za a Gurfanar da Mutane 400 a Gaban Kotun Tarayya da ke Abuja
X whatsapp