Home SIYASA Abinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu – Gwamnan Ahmed Aliyu 

Abinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu – Gwamnan Ahmed Aliyu 

Abinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu – Gwamnan Ahmed Aliyu 

 

Gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, ya ce shaye-shayen miyagun ƙwayoyi ne ke haddasa kusan kashi 80 na matsalolin tsaro da jihar ke fuskanta.

Aliyu ya ce mafi yawan masu aikata laifuka a jihar da ƴanbindiga na amfani da miyagun ƙwayoyi kafin su aikata ta’addanci.

Gwamnan wanda mataimakinsa, Idris Mohammed Gobir, ya wakilta ya bayyana hakan ne a yayin wani taron lacca da aka shirya domin tunawa da ranar yaƙi da shan miyagun ƙwayoyi da safararsu.

“Kashi 80 cikin 100 na matsalolin tsaron da ke addabar jiharmu suna da alaƙa da shan miyagun ƙwayoyi. Waɗannan mutane na amfani da ƙwayoyi masu haɗari. Mutumin da yake cikin hankalinsa ba zai dubi wani ɗan adam ya kashe shi ba,” in ji shi.

Aliyu ya kuma buƙaci matasa su guji shiga harkar shaye-shaye da safarar miyagun ƙwayoyi domin samun damar zama shugabanni da fitattun mutane a nan gaba.

Ya ce gwamnatin jihar ta kafa ofishin babban mataimaki na musamman kan daƙile shaye-shayen miyagun ƙwayoyi domin jagorantar shirye-shiryen wayar da kan jama’a.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp