Home Taska Rundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a Filato

Rundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a Filato

Rundunar Soji

Rundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a Filato

 

Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta na rundunar Operation ENDURING PEACE da ke aiki a Jihar Filato sun samu nasarar daƙile wani kwanton ɓauna da ake zargin ’yan bindiga ne suka shirya a ƙaramar hukumar Langtang ta Arewa, yayin wani samame da suka kai bisa bayanan sirri.

Sanarar da rundunar ta fitar ta ce sojojin sun gudanar da aikin ne bayan da aka kama wani da ake zargi dan bindiga ne, wanda ya bayyana wa jami’an tsaro inda ya ɓoye makaminsa a ƙauyen Nwur.

Yayin da dakarun suka tasa ƙeyar wanda ake zargin zuwa wurin domin gano makamin, wasu daga cikin abokan aikinsa suk kai musu hari.

Sai dai sojojin sun mayar da martani cikin gaggawa da karfin wuta, lamarin da ya yi sanadin kashe daya daga cikin maharan.

Wanda aka kama tun farko shi ma ya mutu a yayin musayar wutar da aka yi tsakanin ɓangarorin biyu.

Bayan kammala artabun, sojojin sun binciki yankin inda suka ƙwato makamai, harsasai da sauran kayan da maharan suka bari yayin tserewa.

Rundunar ta ce tana ci gaba da sintirin neman sauran masu aikata lafin tare da jaddada ƙudurinta na hana masu aikata laifuka samun mafaka da kuma kare rayuka da dukiyoyin

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp