Rundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a Filato
Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta na rundunar Operation ENDURING PEACE da ke aiki a Jihar Filato sun samu nasarar daƙile wani kwanton ɓauna da ake zargin ’yan bindiga ne suka shirya a ƙaramar hukumar Langtang ta Arewa, yayin wani samame da suka kai bisa bayanan sirri.
Sanarar da rundunar ta fitar ta ce sojojin sun gudanar da aikin ne bayan da aka kama wani da ake zargi dan bindiga ne, wanda ya bayyana wa jami’an tsaro inda ya ɓoye makaminsa a ƙauyen Nwur.
Read Also:
Yayin da dakarun suka tasa ƙeyar wanda ake zargin zuwa wurin domin gano makamin, wasu daga cikin abokan aikinsa suk kai musu hari.
Sai dai sojojin sun mayar da martani cikin gaggawa da karfin wuta, lamarin da ya yi sanadin kashe daya daga cikin maharan.
Wanda aka kama tun farko shi ma ya mutu a yayin musayar wutar da aka yi tsakanin ɓangarorin biyu.
Bayan kammala artabun, sojojin sun binciki yankin inda suka ƙwato makamai, harsasai da sauran kayan da maharan suka bari yayin tserewa.
Rundunar ta ce tana ci gaba da sintirin neman sauran masu aikata lafin tare da jaddada ƙudurinta na hana masu aikata laifuka samun mafaka da kuma kare rayuka da dukiyoyin










