Home Taska Rundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a Filato

Rundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a Filato

Rundunar Soji

Rundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a Filato

 

Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta na rundunar Operation ENDURING PEACE da ke aiki a Jihar Filato sun samu nasarar daƙile wani kwanton ɓauna da ake zargin ’yan bindiga ne suka shirya a ƙaramar hukumar Langtang ta Arewa, yayin wani samame da suka kai bisa bayanan sirri.

Sanarar da rundunar ta fitar ta ce sojojin sun gudanar da aikin ne bayan da aka kama wani da ake zargi dan bindiga ne, wanda ya bayyana wa jami’an tsaro inda ya ɓoye makaminsa a ƙauyen Nwur.

Yayin da dakarun suka tasa ƙeyar wanda ake zargin zuwa wurin domin gano makamin, wasu daga cikin abokan aikinsa suk kai musu hari.

Sai dai sojojin sun mayar da martani cikin gaggawa da karfin wuta, lamarin da ya yi sanadin kashe daya daga cikin maharan.

Wanda aka kama tun farko shi ma ya mutu a yayin musayar wutar da aka yi tsakanin ɓangarorin biyu.

Bayan kammala artabun, sojojin sun binciki yankin inda suka ƙwato makamai, harsasai da sauran kayan da maharan suka bari yayin tserewa.

Rundunar ta ce tana ci gaba da sintirin neman sauran masu aikata lafin tare da jaddada ƙudurinta na hana masu aikata laifuka samun mafaka da kuma kare rayuka da dukiyoyin

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Jami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga PantamiGazawar Demarketing: Yadda Sukar Rarara Mai Cike da Kiyayya ga Pantami Ya Rushe Daga Yushau A. ShuaibƘungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin AikiDakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da suƳan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari'a da ke Jihar Katsina
X whatsapp