Home Taska Jami’an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a...

Jami’an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar Kebbi

Jami’an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar Kebbi

 

Rundunar ƴansandan Najeriya ta tabbatar da mutuwar jami’anta 10 a wani artabu da ƴanbindiga a jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin Najeriya.

Rundunar ta ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 9:25 na safiyar Litinin 10 ga watan Agusta, a yankin Rafin Makuku da ke ƙaramar hukumar Sakaba.

A sanarwar da kakakin rundunar na ƙasa CSP Ani Iniedu ya fitar, ya ce jami’anta sun tare ƴanbindigar ɗauke da muggan makamai ne yayin da suke ƙoƙarin wucewa daga jihar Zamfara zuwa Kebbi, inda suka yi musayar wuta.

Rundunar ta ce an kashe aƙalla ƴanbindiga 17 tare da lalata babura huɗu na maharan.

Sai dai jami’an ƴansanda 10 sun rasa rayukansu a artabun, yayin da wasu biyu suka samu raunuka inda a yanzu suke samun kulawa.

Rundunar ta kuma ce wasu fararen hula biyu sun mutu a yayin musayar wutar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp