Home Taska Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya 

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya 

Rundunar Soji

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya

 

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya yaba wa jami’an tsaro bayan nasarar da suka samu wajen ceto mutane 308 da ƴanbindiga suka sace a jihohin Kwara da Neja da ke arewa ta tsakiya.

A cikin mutanen da aka ceto, 163 an sace su ne daga yankin Woro da ke ƙaramar hukumar Kaiama a jihar Kwara, yayin da 145 kuma aka sace su daga jihar Neja.

A wata sanarwa da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga, ya fitar, an ce an ceto mutanen ne daga dajin Kainji Lake National Park da ke ƙaramar hukumar New Bussa a jihar Neja.

Sanarwar ta ce an gudanar da aikin ne bisa sahihan bayanan sirri, tare da haɗin gwiwar Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci ta Ƙasa (NCTC), Rundunar Sojin Najeriya, Hukumar DSS da kuma ‘Yan Sandan Najeriya.

“Wannan shi ne mafi girman aikin ceto mutane da aka taɓa gudanarwa cikin rana guda ta hannun jami’an tsaron haɗin gwiwa,” a cewar shugaban ƙasa.

Tinubu ya yaba da jarumtaka da haɗin kan jami’an tsaron, inda ya ce nasarar ta nuna yadda ayyukan tsaro da tattara bayanan sirri ke ƙara inganta.

Mutanen da aka ceto na karɓar kulawar gaggawa a asibitin Wawa Cantonment, kafin daga bisani a miƙa su ga gwamnatocin jihohinsu domin ci gaba da kula da su da kuma haɗa su da iyalansu.

Shugaban ya sake tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da ɗaukar matakan da suka dace domin kawar da matsalolin tsaro da dawo da zaman lafiya a faɗin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Meyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu MohammedJami'an Tsaro Sun Kai Farmaki Sansanin IPOB/ESN, Sun Kawar da 'Yan Ta'adda 6 a AnambraOperation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Lalata Motocin Yaƙi Guda Biyu na ISWAP, Sannan Ya Kawar da Ƴan Ta'adda da Dama a BornoMai fafutuka Mahdi Shehu ya yi Gargadin Cewa Kudirin Dokar NGO Zai iya Shafar Masallatai, Coci, da Ƙungiyoyin ɗalibaiRikicin Karkashin Mulkin APC a Katsina: ADC na Radda da CSO Har Yanzu Suna Tsare a Hannun Masu ba Tinubu Shawara, MasariAnambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron Hanya
X whatsapp