Home Taska Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya 

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya 

Rundunar Soji

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya

 

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya yaba wa jami’an tsaro bayan nasarar da suka samu wajen ceto mutane 308 da ƴanbindiga suka sace a jihohin Kwara da Neja da ke arewa ta tsakiya.

A cikin mutanen da aka ceto, 163 an sace su ne daga yankin Woro da ke ƙaramar hukumar Kaiama a jihar Kwara, yayin da 145 kuma aka sace su daga jihar Neja.

A wata sanarwa da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga, ya fitar, an ce an ceto mutanen ne daga dajin Kainji Lake National Park da ke ƙaramar hukumar New Bussa a jihar Neja.

Sanarwar ta ce an gudanar da aikin ne bisa sahihan bayanan sirri, tare da haɗin gwiwar Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci ta Ƙasa (NCTC), Rundunar Sojin Najeriya, Hukumar DSS da kuma ‘Yan Sandan Najeriya.

“Wannan shi ne mafi girman aikin ceto mutane da aka taɓa gudanarwa cikin rana guda ta hannun jami’an tsaron haɗin gwiwa,” a cewar shugaban ƙasa.

Tinubu ya yaba da jarumtaka da haɗin kan jami’an tsaron, inda ya ce nasarar ta nuna yadda ayyukan tsaro da tattara bayanan sirri ke ƙara inganta.

Mutanen da aka ceto na karɓar kulawar gaggawa a asibitin Wawa Cantonment, kafin daga bisani a miƙa su ga gwamnatocin jihohinsu domin ci gaba da kula da su da kuma haɗa su da iyalansu.

Shugaban ya sake tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da ɗaukar matakan da suka dace domin kawar da matsalolin tsaro da dawo da zaman lafiya a faɗin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga PantamiGazawar Demarketing: Yadda Sukar Rarara Mai Cike da Kiyayya ga Pantami Ya Rushe Daga Yushau A. ShuaibƘungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin AikiDakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da suƳan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari'a da ke Jihar KatsinaBa ma Goyon Bayan a Riƙa Tura Sojoji Domin Aikin Tsaro a Lokacin Zaɓe - INECJam'iyyar NDC ta Buƙaci Sanata Hanga da Gaya da su Sake Tunani Kan Sauya SheƙaYan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata MatarsaMutane 15 Sun Mutu a Sabon Harin Yan Bindiga a Jihar Benue Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi MataimakinsaJami'an Tsaro Sun Kuɓutar da Mutane 32 Yayin da 4 Suka Mutu a Jihar Sokoto 
X whatsapp