Home Taska Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya 

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya 

Rundunar Soji

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya

 

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya yaba wa jami’an tsaro bayan nasarar da suka samu wajen ceto mutane 308 da ƴanbindiga suka sace a jihohin Kwara da Neja da ke arewa ta tsakiya.

A cikin mutanen da aka ceto, 163 an sace su ne daga yankin Woro da ke ƙaramar hukumar Kaiama a jihar Kwara, yayin da 145 kuma aka sace su daga jihar Neja.

A wata sanarwa da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga, ya fitar, an ce an ceto mutanen ne daga dajin Kainji Lake National Park da ke ƙaramar hukumar New Bussa a jihar Neja.

Sanarwar ta ce an gudanar da aikin ne bisa sahihan bayanan sirri, tare da haɗin gwiwar Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci ta Ƙasa (NCTC), Rundunar Sojin Najeriya, Hukumar DSS da kuma ‘Yan Sandan Najeriya.

“Wannan shi ne mafi girman aikin ceto mutane da aka taɓa gudanarwa cikin rana guda ta hannun jami’an tsaron haɗin gwiwa,” a cewar shugaban ƙasa.

Tinubu ya yaba da jarumtaka da haɗin kan jami’an tsaron, inda ya ce nasarar ta nuna yadda ayyukan tsaro da tattara bayanan sirri ke ƙara inganta.

Mutanen da aka ceto na karɓar kulawar gaggawa a asibitin Wawa Cantonment, kafin daga bisani a miƙa su ga gwamnatocin jihohinsu domin ci gaba da kula da su da kuma haɗa su da iyalansu.

Shugaban ya sake tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da ɗaukar matakan da suka dace domin kawar da matsalolin tsaro da dawo da zaman lafiya a faɗin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dr Lawan Sani: Yadda Masanin Tsaron Intanet Ya Zama Sarkin Gumel: Daga Shuaib S. AgakaAllah ne Kawai Zai Iya Hana Tinubu Cin Nasara a 2027 — Datti"Dangantakar Farar Hula da Sojoji Itace Mabuɗi ga Tsaron Ƙasa da Shugabanci Nagari" — Tsohon CDS IraborRundunar Sojin Najeriya ta Binciki Zargin Cin Zarafin Jima'i da Aka yi wa Kyaftin a JosBabban Jami’in EFCC na Fuskantar Zarge-Zargen Cin Hanci da Dukiyar da ba a San Asalinta baƳan Sandan Legas Sun Kama Mutum 4 da Ake Zargi da Fashin Daji, Sun Kwato Wayoyin Hannu 25, Kwamfutoci da Kayan Ado na ZinareRundunar Sojin Ruwa Ta Rusa Wuraren Tace Mai Ba bisa Ka’ida Ba, Ta Kwato Lita 350 na AGO a Rivers2027: Yahaya Bello Ya Tara Masu Daidaita Ayyuka na A4A a Arewa ta Tsakiya Domin sake Zaban TinubuSojoji Sun Kama Mutum 2 da ake Zargi da Taimakawa Ƴan Ta’adda, Sun Kwace Kayayyakin Babur a YobePDP Ta Yi Gargadi Kan Zargin Tattara Katunan Zabe PVC da Bayanan Asusun Banki a GombeRundunar Sojojin Najeriya ta Sauya Manyan Janarori Zuwa Muhimman Mukamai na Aiki da DabaruHukumar INEC za ta ƙaddamar da Na’urar Bibiyar shirye-shiryen Zaɓen 2027 kai TsayeDaliban Tallafin Horarwa na Prnigeria Sun Ziyarci Emirate FM, Sun Samu Kyawawan Bayani Kan Watsa Labarai na DijitalNSCIA ta yi Allah Wadai da Nuna Bambancin Addini a Ci gaba da Tsare El-RufaiSarkin Ilorin Ya Yaba da Tallafin Horarwa na PRNigeria Wajen Shirya Masu Watsa Labarai na Nan Gaba
X whatsapp