Shahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar Osun
Shahararren mawaƙin Najeriya, Davido ya rubuta wa shugaban Amurka, Donald Trump wasiƙa domin jawo hankalinsa kan halin siyasar da ake ciki a jihar Osun.
Ya rubuta wasiƙar ne a yayin da ake tunkarar zaɓen gwamnan jihar a ranar Asabar inda ya buƙaci shugaban na Amurka ya sanya ido sosai kan zaɓen da za a gudanar.
Read Also:
A saƙon da ya wallafa a shafinsa na X, Davido ya bayyana damuwarsa kan yiwuwar tashin hankali da wasu yiwuwar kawo cikas ga zaɓen cikin lumana da adalci.
“Mutanen Osun suna da ƴancinsu da na ƙundin tsarin mulki ya basu na kaɗa ƙuri’a, cikin lumana kuma ba tare da tsoro ba,” in ji shi.
Mawaƙin ya kuma yi kira ga Amurka da ƙasashen duniya da su mai da hankali kan zaɓen, yana mai cewa, “Ba ma son a zubar da jini. Ba ma son tsoratar da jama’a. Abin da muke so shi ne zaman lafiya, gaskiya da kuma sahihin zaɓe.”












