Home Labarai Jami’an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji

Jami’an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji

Jami’an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji

 

Jami’an hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya (DSS) sun kama tsohon ministan kimiyya da fasaha, Uche Nnaji, a safiyar ranar Laraba a filin jirgin saman Akanu Ibiam da ke Enugu.

Rahotanni sun ce an kama Nnaji ne yayin da yake shirin hawa jirgi zuwa Abuja.

Wasu majiyoyin tsaro sun ce jami’an DSS sun kama shi ne bisa buƙatar Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta ICPC, wadda ake zargin tana bincikensa kan zargin amfani da takardun bogi

Daga bisani an miƙa shi ga hukumar ICPC, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Majiyoyin sun kuma ce ICPC ta taɓa gayyatar tsohon ministan sau da dama bayan samun koke-koke kan yadda ya gudanar da ma’aikatar da yake jagoranta, lamarin da ya sa ta nemi taimakon DSS domin cafke shi.

Uche Nnaji ya yi murabus daga muƙaminsa a ranar 7 ga Oktoban 2025, bayan ce-ce-ku-cen da suka biyo bayan takardun karatunsa daga Jami’ar Najeriya (UNN) da kuma takardar kammala bautar ƙasa ta NYSC.

A lokacin, ya ce murabus ɗin ba yana nufin amincewa da laifin da ake zarginsa da shi ba ne, illa dai mataki ne na mutunta tsarin shari’a, inda ya ce zarge-zargen suna da alaƙa da siyasa.

A watan Nuwamban 2025, ya shigar da ƙara a Babbar Kotun Tarayya domin tilasta wa Jami’ar da shugaban jami’ar su ba shi kwafin cikakken bayanan karatunsa.

Lamarin ya sake ɗaukar sabon salo ne bayan jam’iyyar PDP ta zaɓi Uche Nnaji a matsayin ɗan takararta na gwamnan jihar Enugu a zaɓen 2027.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar ShekaraShugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta'addanciBinciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko HaramHukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar Yan SandaMutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto 
X whatsapp