Home Taska Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta’adda

Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta’adda

Rundunar Soji

Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta’adda

 

Dakarun Rundunar sojoji na Operation FANSAN YAMMA sun bankaɗo wata masana’antar ƙera bindigogi haramtacciya da ake zargin tana samar da makamai ga ’yan ta’adda a Jihar Kebbi.

Mai magana da yawun rundunar, Laftanar Kanar Aliyu Danja ya ce dakarun sun kai samamen ne bayan samun sahihan bayanan sirri kan wani wuri da ake amfani da shi wajen ƙera da rarraba bindigogi.

A yayin binciken da aka gudanar, an ƙwato bindigogin AK-47 guda biyar da aka ƙera a cikin gida, sannan an kama mutum biyu da ake zargin masu ƙera da safarar makaman ne.

Ya ce, an gudanar da aikin ne tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro, yana mai cewa hakan wani gagarumin ci gaba ne a ƙoƙarin da ake yi na daƙile yaɗuwar makamai ba bisa ƙa’ida ba da kuma dakile hanyoyin da ’yan ta’adda ke samun kayan aiki.

A cewarsa, waɗanda aka kama na tsare a hannun sojoji domin ci gaba da bincike, yayin da ake farautar sauran mambobin ƙungiyar da masu ɗaukar nauyinsu.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a Jihar
X whatsapp