Home Taska Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta’adda

Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta’adda

Rundunar Soji

Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta’adda

 

Dakarun Rundunar sojoji na Operation FANSAN YAMMA sun bankaɗo wata masana’antar ƙera bindigogi haramtacciya da ake zargin tana samar da makamai ga ’yan ta’adda a Jihar Kebbi.

Mai magana da yawun rundunar, Laftanar Kanar Aliyu Danja ya ce dakarun sun kai samamen ne bayan samun sahihan bayanan sirri kan wani wuri da ake amfani da shi wajen ƙera da rarraba bindigogi.

A yayin binciken da aka gudanar, an ƙwato bindigogin AK-47 guda biyar da aka ƙera a cikin gida, sannan an kama mutum biyu da ake zargin masu ƙera da safarar makaman ne.

Ya ce, an gudanar da aikin ne tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro, yana mai cewa hakan wani gagarumin ci gaba ne a ƙoƙarin da ake yi na daƙile yaɗuwar makamai ba bisa ƙa’ida ba da kuma dakile hanyoyin da ’yan ta’adda ke samun kayan aiki.

A cewarsa, waɗanda aka kama na tsare a hannun sojoji domin ci gaba da bincike, yayin da ake farautar sauran mambobin ƙungiyar da masu ɗaukar nauyinsu.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar ShekaraShugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta'addanciBinciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko HaramHukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar Yan SandaMutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto 
X whatsapp