Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta’adda
Dakarun Rundunar sojoji na Operation FANSAN YAMMA sun bankaɗo wata masana’antar ƙera bindigogi haramtacciya da ake zargin tana samar da makamai ga ’yan ta’adda a Jihar Kebbi.
Mai magana da yawun rundunar, Laftanar Kanar Aliyu Danja ya ce dakarun sun kai samamen ne bayan samun sahihan bayanan sirri kan wani wuri da ake amfani da shi wajen ƙera da rarraba bindigogi.
Read Also:
A yayin binciken da aka gudanar, an ƙwato bindigogin AK-47 guda biyar da aka ƙera a cikin gida, sannan an kama mutum biyu da ake zargin masu ƙera da safarar makaman ne.
Ya ce, an gudanar da aikin ne tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro, yana mai cewa hakan wani gagarumin ci gaba ne a ƙoƙarin da ake yi na daƙile yaɗuwar makamai ba bisa ƙa’ida ba da kuma dakile hanyoyin da ’yan ta’adda ke samun kayan aiki.
A cewarsa, waɗanda aka kama na tsare a hannun sojoji domin ci gaba da bincike, yayin da ake farautar sauran mambobin ƙungiyar da masu ɗaukar nauyinsu.










