Home Taska Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto 

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto 

'Yan Bindiga

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto 

 

An samu rahoton kashe Babban Limamin ƙauyen Talluje da ke Ƙaramar Hukumar Bodinga a Jihar Sakkwato ranar Laraba, bayan da ’yan bindiga suka kai hari a Talluje da maƙwabtanta ƙauyen Chofi.

Lamarin ya yi sanadin mutuwar wasu mazauna ƙauyen guda biyu tare da tilasta wa ɗaruruwan mutane tserewa daga gidajensu.

Harin, wanda ya fara da misalin ƙarfe 4:00 na yamma, ya auka wa unguwanni biyu da ke Gundumar Danchadi, kuma ya shafe kusan sa’o’i biyu ana fafatawa.

Wannan lamari ya kawo adadin sanadin rasa rayukan Manyan limamai guda uku da rahotanni suka ce ’yan bindiga sun kashe a Jihar Sakkwato cikin ‘yan makonnin da suka gabata.

Majiyoyi daga yankin sun shaida wa wakilinmu cewa, maharan sun kai hare-hare na bai-ɗaya a lokaci guda a duka unguwanni biyu, inda suka riƙa harbi ba ƙaƙƙautawa kafin su tsere da adadin dabbobin da ba a tantance ba waɗanda suka sace.

“Hare-haren sun fara ne da misalin ƙarfe 4:00 na yamma kuma suka ci gaba har zuwa kusan ƙarfe 6:00 na yamma. ’Yan bindigar sun kashe Babban Limamin Talluje da wasu mutane biyu waɗanda har yanzu ba a tantance ko su wane ne ba,” in ji wani shugaban unguwa a Danchadi.

Ya ƙara da cewa, hare-haren sun haddasa gudun hijira, inda mazauna yankin, musamman mata da ƙananan yara, suka tsere da ƙafafunsu zuwa wurare mafi aminci a Danchadi da garin Bodinga.

“Yayin da nake magana da kai, mutane da yawa suna tserewa daga unguwanninsu ɗauke da kayayyakinsu bayan sun tsere daga asalin ƙauyukan da abin ya shafa,” in ji majiyar.

Wani mazaunin yankin ya tabbatar da cewa, maharan sun kwashe dabbobi masu yawa, kodayake ba a iya tantance ainihin adadin su ba nan take.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 2 Sun Mutu Bayan Hatsarin Tankar Mai a IbadanƘungiyar MURIC ta Zargi INEC da Hana Mata Masu Hijabi Kaɗa ƙuri’arsu a Zaɓen Jihar Osun Babu Dan Takara ko Tikiti da zai iya Doke Namu a Zaɓen 2027 - Kwankwaso Mutane 5 Sun Mutu Bayan Kwale-Kwale ya Kife a Jihar Neja Nijar ta ƙulla Yarjejeniyar Gina Matatar Mai da Kamfani a CanadaMabiya Addinai Biyu a Najeriya Sun Sanya Hannu Kan Sabuwar YarjejeniyaAn Kashe Matashi Kan Murfin Tayar Adaidaita Sahu a KanoMutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin Gargajiya
X whatsapp