Home Taska Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto 

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto 

'Yan Bindiga

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto 

 

An samu rahoton kashe Babban Limamin ƙauyen Talluje da ke Ƙaramar Hukumar Bodinga a Jihar Sakkwato ranar Laraba, bayan da ’yan bindiga suka kai hari a Talluje da maƙwabtanta ƙauyen Chofi.

Lamarin ya yi sanadin mutuwar wasu mazauna ƙauyen guda biyu tare da tilasta wa ɗaruruwan mutane tserewa daga gidajensu.

Harin, wanda ya fara da misalin ƙarfe 4:00 na yamma, ya auka wa unguwanni biyu da ke Gundumar Danchadi, kuma ya shafe kusan sa’o’i biyu ana fafatawa.

Wannan lamari ya kawo adadin sanadin rasa rayukan Manyan limamai guda uku da rahotanni suka ce ’yan bindiga sun kashe a Jihar Sakkwato cikin ‘yan makonnin da suka gabata.

Majiyoyi daga yankin sun shaida wa wakilinmu cewa, maharan sun kai hare-hare na bai-ɗaya a lokaci guda a duka unguwanni biyu, inda suka riƙa harbi ba ƙaƙƙautawa kafin su tsere da adadin dabbobin da ba a tantance ba waɗanda suka sace.

“Hare-haren sun fara ne da misalin ƙarfe 4:00 na yamma kuma suka ci gaba har zuwa kusan ƙarfe 6:00 na yamma. ’Yan bindigar sun kashe Babban Limamin Talluje da wasu mutane biyu waɗanda har yanzu ba a tantance ko su wane ne ba,” in ji wani shugaban unguwa a Danchadi.

Ya ƙara da cewa, hare-haren sun haddasa gudun hijira, inda mazauna yankin, musamman mata da ƙananan yara, suka tsere da ƙafafunsu zuwa wurare mafi aminci a Danchadi da garin Bodinga.

“Yayin da nake magana da kai, mutane da yawa suna tserewa daga unguwanninsu ɗauke da kayayyakinsu bayan sun tsere daga asalin ƙauyukan da abin ya shafa,” in ji majiyar.

Wani mazaunin yankin ya tabbatar da cewa, maharan sun kwashe dabbobi masu yawa, kodayake ba a iya tantance ainihin adadin su ba nan take.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a Jihar
X whatsapp