Home Labarai Juyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva 

Juyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva 

Juyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva 

 

Hukumar Tsaro ta Farin Kaya ta Najeriya, DSS, ta gurfanar da wasu mutum biyar a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja bisa zarginsu da ɓoye bayanai kan inda tsohon gwamnan jihar Bayelsa, Timipre Sylva yake.

DSS ta kuma zarge su da haɗa baki wajen aikata laifi ta hanyar ɓoye inda Mista Sylva yake, wanda ta ce mutum ne da hukumomi ke nema ruwa a jallo.

Dukkan waɗanda ake tuhuma sun musanta zarge-zargen da aka karanta musu a gaban kotu.

Lauyan DSS, Emmanuel Orubor, ya roƙi kotun ta sanya ranar da za a fara sauraron shari’ar, inda hukumar za ta gabatar da shaidu.

Sai dai lauyan wasu daga cikin waɗanda ake tuhuma, Sanusi Musa, SAN, ya nemi a ba su beli bayan gabatar da hujjoji.

Mai shari’a Peter Lifu ya umarci magatakardar kotu da a tantance waɗanda suka tsaya wa waɗanda ake tuhuma har sai an cika sharuddan beli, inda kotun ta ba da umarnin a ci gaba da tsare su a gidan gyaran hali na Kuje.

Kotun ta ɗage ci gaba da sauraron shari’ar zuwa ranar 22 ga Yuli.

Ana zargin Mista Sylva, tsohon ministan man fetur, da kasancewa jagoran yunkurin juyin mulki da ake zargin an shirya wa Shugaba Bola Tinubu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar ShekaraShugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta'addanciBinciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko HaramHukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar Yan SandaMutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto 
X whatsapp