Home Labarai Juyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva 

Juyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva 

Juyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva 

 

Hukumar Tsaro ta Farin Kaya ta Najeriya, DSS, ta gurfanar da wasu mutum biyar a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja bisa zarginsu da ɓoye bayanai kan inda tsohon gwamnan jihar Bayelsa, Timipre Sylva yake.

DSS ta kuma zarge su da haɗa baki wajen aikata laifi ta hanyar ɓoye inda Mista Sylva yake, wanda ta ce mutum ne da hukumomi ke nema ruwa a jallo.

Dukkan waɗanda ake tuhuma sun musanta zarge-zargen da aka karanta musu a gaban kotu.

Lauyan DSS, Emmanuel Orubor, ya roƙi kotun ta sanya ranar da za a fara sauraron shari’ar, inda hukumar za ta gabatar da shaidu.

Sai dai lauyan wasu daga cikin waɗanda ake tuhuma, Sanusi Musa, SAN, ya nemi a ba su beli bayan gabatar da hujjoji.

Mai shari’a Peter Lifu ya umarci magatakardar kotu da a tantance waɗanda suka tsaya wa waɗanda ake tuhuma har sai an cika sharuddan beli, inda kotun ta ba da umarnin a ci gaba da tsare su a gidan gyaran hali na Kuje.

Kotun ta ɗage ci gaba da sauraron shari’ar zuwa ranar 22 ga Yuli.

Ana zargin Mista Sylva, tsohon ministan man fetur, da kasancewa jagoran yunkurin juyin mulki da ake zargin an shirya wa Shugaba Bola Tinubu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp