Home Labarai Juyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva 

Juyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva 

Juyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva 

 

Hukumar Tsaro ta Farin Kaya ta Najeriya, DSS, ta gurfanar da wasu mutum biyar a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja bisa zarginsu da ɓoye bayanai kan inda tsohon gwamnan jihar Bayelsa, Timipre Sylva yake.

DSS ta kuma zarge su da haɗa baki wajen aikata laifi ta hanyar ɓoye inda Mista Sylva yake, wanda ta ce mutum ne da hukumomi ke nema ruwa a jallo.

Dukkan waɗanda ake tuhuma sun musanta zarge-zargen da aka karanta musu a gaban kotu.

Lauyan DSS, Emmanuel Orubor, ya roƙi kotun ta sanya ranar da za a fara sauraron shari’ar, inda hukumar za ta gabatar da shaidu.

Sai dai lauyan wasu daga cikin waɗanda ake tuhuma, Sanusi Musa, SAN, ya nemi a ba su beli bayan gabatar da hujjoji.

Mai shari’a Peter Lifu ya umarci magatakardar kotu da a tantance waɗanda suka tsaya wa waɗanda ake tuhuma har sai an cika sharuddan beli, inda kotun ta ba da umarnin a ci gaba da tsare su a gidan gyaran hali na Kuje.

Kotun ta ɗage ci gaba da sauraron shari’ar zuwa ranar 22 ga Yuli.

Ana zargin Mista Sylva, tsohon ministan man fetur, da kasancewa jagoran yunkurin juyin mulki da ake zargin an shirya wa Shugaba Bola Tinubu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
An Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga PantamiGazawar Demarketing: Yadda Sukar Rarara Mai Cike da Kiyayya ga Pantami Ya Rushe Daga Yushau A. ShuaibƘungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin AikiDakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da suƳan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari'a da ke Jihar KatsinaBa ma Goyon Bayan a Riƙa Tura Sojoji Domin Aikin Tsaro a Lokacin Zaɓe - INEC
X whatsapp