Home Labarai Juyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva 

Juyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva 

Juyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva 

 

Hukumar Tsaro ta Farin Kaya ta Najeriya, DSS, ta gurfanar da wasu mutum biyar a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja bisa zarginsu da ɓoye bayanai kan inda tsohon gwamnan jihar Bayelsa, Timipre Sylva yake.

DSS ta kuma zarge su da haɗa baki wajen aikata laifi ta hanyar ɓoye inda Mista Sylva yake, wanda ta ce mutum ne da hukumomi ke nema ruwa a jallo.

Dukkan waɗanda ake tuhuma sun musanta zarge-zargen da aka karanta musu a gaban kotu.

Lauyan DSS, Emmanuel Orubor, ya roƙi kotun ta sanya ranar da za a fara sauraron shari’ar, inda hukumar za ta gabatar da shaidu.

Sai dai lauyan wasu daga cikin waɗanda ake tuhuma, Sanusi Musa, SAN, ya nemi a ba su beli bayan gabatar da hujjoji.

Mai shari’a Peter Lifu ya umarci magatakardar kotu da a tantance waɗanda suka tsaya wa waɗanda ake tuhuma har sai an cika sharuddan beli, inda kotun ta ba da umarnin a ci gaba da tsare su a gidan gyaran hali na Kuje.

Kotun ta ɗage ci gaba da sauraron shari’ar zuwa ranar 22 ga Yuli.

Ana zargin Mista Sylva, tsohon ministan man fetur, da kasancewa jagoran yunkurin juyin mulki da ake zargin an shirya wa Shugaba Bola Tinubu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 2 Sun Mutu Bayan Hatsarin Tankar Mai a IbadanƘungiyar MURIC ta Zargi INEC da Hana Mata Masu Hijabi Kaɗa ƙuri’arsu a Zaɓen Jihar Osun Babu Dan Takara ko Tikiti da zai iya Doke Namu a Zaɓen 2027 - Kwankwaso Mutane 5 Sun Mutu Bayan Kwale-Kwale ya Kife a Jihar Neja Nijar ta ƙulla Yarjejeniyar Gina Matatar Mai da Kamfani a CanadaMabiya Addinai Biyu a Najeriya Sun Sanya Hannu Kan Sabuwar YarjejeniyaAn Kashe Matashi Kan Murfin Tayar Adaidaita Sahu a KanoMutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin Gargajiya
X whatsapp