Home Labarai Majalisar Wakilan Najeriya ta Amince da ƙudirin Dokar Kafa ’Yan sandan Jiha

Majalisar Wakilan Najeriya ta Amince da ƙudirin Dokar Kafa ’Yan sandan Jiha

Benjamin Kalu

Majalisar Wakilan Najeriya ta Amince da ƙudirin Dokar Kafa ’Yan sandan Jiha

 

Majalisar Wakilai a ranar Alhamis ta amince da ƙudirin gyaran tsarin mulki wanda ke neman kafa rundunar ’yan sandan jiha a faɗin ƙasar.

Kudirin, mai taken “ƙudirin Dokar Gyaran Tsarin Mulkin Jamhuriyar Tarayyar Najeriya na shekarar 1999 don samar da Rundunar ’Yan sandan Jiha da sauran al’amura masu alaƙa da hakan (Gyara na Shida), na shekarar 2026,” an amince da shi ne yayin tattaunawa a babban zauren majalisar.

ƙudirin ya tsallake matakin ne bayan da mambobin majalisar suka kaɗa masa ƙuri’a da gagarumin rinjaye biyo bayan gabatar da rahoton da Mataimakin Shugaban Majalisar, kuma Shugaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulki na Majalisar, Benjamin Kalu ya yi.

Hanyar kaɗa ƙuri’a da hannu da majalisar ta yi ta nuna cewa ’yan majalisa 289 ne suka goyi bayan shawarar, mamba guda daya ya ƙi kaɗa ƙuri’a, yayin da babu ko da ɗan majalisa guda da ya ƙeƙashe ƙasa ya ki amincewa da shi.

Gyaran da ake shirin yi yana neman samar da tsarin gudanar da aikin ’yan sanda guda biyu ne da ya ƙunshi ’Yan sandan Tarayya da na Jiha, a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin magance matsalolin tsaro da ke ƙaruwa a ƙasar ta hanyar amfani da raba madafun iko.

A ƙarƙashin shawarar, za a yi gyara ga Sashi na 214 na Tsarin Mulki domin kafa waɗannan rundunoni biyu na ’yan sanda a hukumance.

Majalisar Dokoki ta ƙasa za ta sami ikon ƙayyade tsari, gudanarwa, da kuma ikon ’Yan sandan Tarayya, yayin da kuma za ta gindaya sharuɗan da suka dace don kafa da kuma gudanar da ayyukan rundunonin ’yan sandan jihohi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp