Home Labarai Majalisar Wakilan Najeriya ta Amince da ƙudirin Dokar Kafa ’Yan sandan Jiha

Majalisar Wakilan Najeriya ta Amince da ƙudirin Dokar Kafa ’Yan sandan Jiha

Benjamin Kalu

Majalisar Wakilan Najeriya ta Amince da ƙudirin Dokar Kafa ’Yan sandan Jiha

 

Majalisar Wakilai a ranar Alhamis ta amince da ƙudirin gyaran tsarin mulki wanda ke neman kafa rundunar ’yan sandan jiha a faɗin ƙasar.

Kudirin, mai taken “ƙudirin Dokar Gyaran Tsarin Mulkin Jamhuriyar Tarayyar Najeriya na shekarar 1999 don samar da Rundunar ’Yan sandan Jiha da sauran al’amura masu alaƙa da hakan (Gyara na Shida), na shekarar 2026,” an amince da shi ne yayin tattaunawa a babban zauren majalisar.

ƙudirin ya tsallake matakin ne bayan da mambobin majalisar suka kaɗa masa ƙuri’a da gagarumin rinjaye biyo bayan gabatar da rahoton da Mataimakin Shugaban Majalisar, kuma Shugaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulki na Majalisar, Benjamin Kalu ya yi.

Hanyar kaɗa ƙuri’a da hannu da majalisar ta yi ta nuna cewa ’yan majalisa 289 ne suka goyi bayan shawarar, mamba guda daya ya ƙi kaɗa ƙuri’a, yayin da babu ko da ɗan majalisa guda da ya ƙeƙashe ƙasa ya ki amincewa da shi.

Gyaran da ake shirin yi yana neman samar da tsarin gudanar da aikin ’yan sanda guda biyu ne da ya ƙunshi ’Yan sandan Tarayya da na Jiha, a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin magance matsalolin tsaro da ke ƙaruwa a ƙasar ta hanyar amfani da raba madafun iko.

A ƙarƙashin shawarar, za a yi gyara ga Sashi na 214 na Tsarin Mulki domin kafa waɗannan rundunoni biyu na ’yan sanda a hukumance.

Majalisar Dokoki ta ƙasa za ta sami ikon ƙayyade tsari, gudanarwa, da kuma ikon ’Yan sandan Tarayya, yayin da kuma za ta gindaya sharuɗan da suka dace don kafa da kuma gudanar da ayyukan rundunonin ’yan sandan jihohi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp