Home Taska Amurka ta yi sulhu kan yaƙin da ta ke yi da Iran...

Amurka ta yi sulhu kan yaƙin da ta ke yi da Iran – Trump

Donald trump

Amurka ta yi sulhu kan yaƙin da ta ke yi da Iran – Trump

 

Da yake magana a fadar White House, Trump ya ce “Amurka ta yi sulhu kan yaƙin da ta ke yi da Iran “.

Ya ci gaba da cewa: “Muna kan kammala tattara takardun yarjejeniyar. Za iya kamatawa nan da ƴan kwanaki masu zuwa.”

Trump ya ce “wataƙila za a sanya hannu, mai yiwuwa a Turai” da zarar an kammala tattara takardun, kuma ya kamata a yi “da sauri”.

“Mun ƙulla yarjejeniyar cewa Iran ba za ta taɓa mallakar makamin nukiliya ba, wanda shi ne maƙasudin abin da ya sa muka yi wannan abun don mu samu hakan. Don haka abu ne babba.”

Trump ya ce za a buɗe mashigar Hormuz “da zarar mun sanya hannu”.

Ya kuma ce ya yi magana da shugabannin yankin da suka haɗa da ƙawayen Amurka na ƙasashen Gulf da firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, ya ƙara da cewa: ” Yankin Gabas ta tsakiya baki ɗayanta na mauƙar farin ciki”.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Farashin ɗanyen Mai ya Faɗi Bayan Amurka ta Soke Sabbin Hare-Haren kaiwa IranAmurka ta yi sulhu kan yaƙin da ta ke yi da Iran - TrumpMajalisar Wakilan Najeriya ta Amince da ƙudirin Dokar Kafa ’Yan sandan JihaHukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar NejaMiyagun ƙwayoyi da Makamai: Jami'an Tsaro Sun Kama Mutane 8 a Jihar YobeAbin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar Gombe
X whatsapp