Hukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar Neja
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke wa mutum biyar hukuncin daurin shekara 25 kowannensu bayan samunsu da laifin taimakawa ayyukan ta’addanci da ke da alaƙa da sace ɗalibai.
Harin wanda aka kai makarantar St. Joseph Catholic Church da ke Papiri a Jihar Niger.
A harin da aka kai ranar 21 ga Nuwamban 2025, maharan sun sace ɗalibai da ma’aikata sama da 300. Duk da cewa wasu kusan 50 sun tsere, an yi awon gaba da sama da ɗalibai 250 zuwa dajin Kainji.
Read Also:
Hukumar Tsaro ta DSS ta bi sawun wasu daga cikin waɗanda ake zargi da hannu a lamarin tare da cafke su.
Daga cikin waɗanda aka kama akwai ’yan Najeriya da kuma ’yan Jamhuriyar Nijar biyu.
A lokacin kamen, jami’an DSS sun ƙwato bindigogi ƙirar AK-103 guda 15 da harsasai 1,434 da aka ɓoye a cikin buhuna a wata mota kirar volkswagen Golf.
Mai shari’a Binta Nyako ce ta yanke hukuncin bayan mutanen biyar sun amsa laifuffukan da ake tuhumarsu da su, waɗanda suka haɗa da: haɗa baki da kuma taimakawa ayyukan ta’addanci ta hanyar safarar makamai ga wani da ake zargin mamba ne na Boko Haram.
Kotun ta kuma bayar da umarnin ƙwace motar da aka samu makaman a cikinta tare da mayar da ita mallakin gwamnatin Najeriya.










