Home Taska Hukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar Neja

Hukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar Neja

Hukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar Neja

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke wa mutum biyar hukuncin daurin shekara 25 kowannensu bayan samunsu da laifin taimakawa ayyukan ta’addanci da ke da alaƙa da sace ɗalibai.

Harin wanda aka kai makarantar St. Joseph Catholic Church da ke Papiri a Jihar Niger.

A harin da aka kai ranar 21 ga Nuwamban 2025, maharan sun sace ɗalibai da ma’aikata sama da 300. Duk da cewa wasu kusan 50 sun tsere, an yi awon gaba da sama da ɗalibai 250 zuwa dajin Kainji.

Hukumar Tsaro ta DSS ta bi sawun wasu daga cikin waɗanda ake zargi da hannu a lamarin tare da cafke su.

Daga cikin waɗanda aka kama akwai ’yan Najeriya da kuma ’yan Jamhuriyar Nijar biyu.

A lokacin kamen, jami’an DSS sun ƙwato bindigogi ƙirar AK-103 guda 15 da harsasai 1,434 da aka ɓoye a cikin buhuna a wata mota kirar volkswagen Golf.

Mai shari’a Binta Nyako ce ta yanke hukuncin bayan mutanen biyar sun amsa laifuffukan da ake tuhumarsu da su, waɗanda suka haɗa da: haɗa baki da kuma taimakawa ayyukan ta’addanci ta hanyar safarar makamai ga wani da ake zargin mamba ne na Boko Haram.

Kotun ta kuma bayar da umarnin ƙwace motar da aka samu makaman a cikinta tare da mayar da ita mallakin gwamnatin Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Jami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya 
X whatsapp