Home Taska Hukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar Neja

Hukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar Neja

Hukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar Neja

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke wa mutum biyar hukuncin daurin shekara 25 kowannensu bayan samunsu da laifin taimakawa ayyukan ta’addanci da ke da alaƙa da sace ɗalibai.

Harin wanda aka kai makarantar St. Joseph Catholic Church da ke Papiri a Jihar Niger.

A harin da aka kai ranar 21 ga Nuwamban 2025, maharan sun sace ɗalibai da ma’aikata sama da 300. Duk da cewa wasu kusan 50 sun tsere, an yi awon gaba da sama da ɗalibai 250 zuwa dajin Kainji.

Hukumar Tsaro ta DSS ta bi sawun wasu daga cikin waɗanda ake zargi da hannu a lamarin tare da cafke su.

Daga cikin waɗanda aka kama akwai ’yan Najeriya da kuma ’yan Jamhuriyar Nijar biyu.

A lokacin kamen, jami’an DSS sun ƙwato bindigogi ƙirar AK-103 guda 15 da harsasai 1,434 da aka ɓoye a cikin buhuna a wata mota kirar volkswagen Golf.

Mai shari’a Binta Nyako ce ta yanke hukuncin bayan mutanen biyar sun amsa laifuffukan da ake tuhumarsu da su, waɗanda suka haɗa da: haɗa baki da kuma taimakawa ayyukan ta’addanci ta hanyar safarar makamai ga wani da ake zargin mamba ne na Boko Haram.

Kotun ta kuma bayar da umarnin ƙwace motar da aka samu makaman a cikinta tare da mayar da ita mallakin gwamnatin Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp