Home Taska Hukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar Neja

Hukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar Neja

Hukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar Neja

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke wa mutum biyar hukuncin daurin shekara 25 kowannensu bayan samunsu da laifin taimakawa ayyukan ta’addanci da ke da alaƙa da sace ɗalibai.

Harin wanda aka kai makarantar St. Joseph Catholic Church da ke Papiri a Jihar Niger.

A harin da aka kai ranar 21 ga Nuwamban 2025, maharan sun sace ɗalibai da ma’aikata sama da 300. Duk da cewa wasu kusan 50 sun tsere, an yi awon gaba da sama da ɗalibai 250 zuwa dajin Kainji.

Hukumar Tsaro ta DSS ta bi sawun wasu daga cikin waɗanda ake zargi da hannu a lamarin tare da cafke su.

Daga cikin waɗanda aka kama akwai ’yan Najeriya da kuma ’yan Jamhuriyar Nijar biyu.

A lokacin kamen, jami’an DSS sun ƙwato bindigogi ƙirar AK-103 guda 15 da harsasai 1,434 da aka ɓoye a cikin buhuna a wata mota kirar volkswagen Golf.

Mai shari’a Binta Nyako ce ta yanke hukuncin bayan mutanen biyar sun amsa laifuffukan da ake tuhumarsu da su, waɗanda suka haɗa da: haɗa baki da kuma taimakawa ayyukan ta’addanci ta hanyar safarar makamai ga wani da ake zargin mamba ne na Boko Haram.

Kotun ta kuma bayar da umarnin ƙwace motar da aka samu makaman a cikinta tare da mayar da ita mallakin gwamnatin Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp