Home Taska Miyagun ƙwayoyi da Makamai: Jami’an Tsaro Sun Kama Mutane 8 a Jihar...

Miyagun ƙwayoyi da Makamai: Jami’an Tsaro Sun Kama Mutane 8 a Jihar Yobe

Arrest

Miyagun ƙwayoyi da Makamai: Jami’an Tsaro Sun Kama Mutane 8 a Jihar Yobe

Rundunar ’yan sandan jihar Yobe ta kama mutane takwas bisa zargin laifukan da suka shafi miyagun ƙwayoyi, sannan ta ƙwato makamai da dama a sassa daban-daban na jihar.

Kamen waɗanda ake zargi, ya biyo bayan ci gaba da tsare-tsaren hana aikata laifuka da kuma daƙile su ta hanyar yin sintiri mai ƙarfi, da kai samame a maɓoyar masu laifi da wuraren ɓatagari da ’yan sanda ƙarƙashin jagorancin leƙen asiri a faɗin jihar ke yi.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Dungus Abdulkarim ne ya bayyana hakan, inda ya ce baya ga waɗannan ƙoƙarin, sabuwar rundunar da aka kafa a ƙarƙashin sabon sashin mayar da martani kan laifuka ( VCRU), makonni biyu bayan ƙaddamar da ita, ta fara gudanar da ayyuka na dare da rana kuma ta samu ci gaba tare da kama mutane takwas da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi da kuma waɗanda ake zargi da aikata laifuka masu tayar da hankali.

Ya ƙara da cewa, “A ranar 9 ga Yuni, 2026, da misalin ƙarfe 18:00 na safe, jami’an rundunar VCRU, waɗanda ke aiki bisa bayanan sirri sun gudanar da wani samame a sanannen sansanin ’yan sanda na New Marte Ghetto da ke Damaturu.”

Ya ce, an kama Usman Hassan, wanda aka fi sani da Bapani, mai shekara 20, da ke da tarin wiwi da kuma tarin takardun rubutattu na ɗaliban Jami’ar Jihar Yobe.

An kuma kama Bukar Sale, wanda aka fi sani da Benzima, mai shekara 18, ɗauke da wasu miyagun ƙwayoyi da kuma tabar wiwi.

Sauran mutane shida da ake zargi sun haɗa da: Adamu, mai shekara 18, Hassan Abdullahi, mai shekara 20, Ibrahim Ibrahim, wanda aka fi sani da Bomboy, mai shekara 20, Usman Sale, wanda aka fi sani da Ado Gonja, mai shekara 21, Mohammed Salisu, wanda aka fi sani da RP Damboa, mai shekara 25, da Bako Mohammed, wanda aka fi sani da Balande, mai shekara 18, da ake zargin su da aikata mabanbanta laifuka.

Ya ƙara da cewa, dukkan waɗanda ake zargin mazauna unguwar Pompomari Sabon Kwalta ne, a cikin garin Damaturu. Inda ya ce a lokacin samamen, an gano wasu abubuwa da suka haɗa da tabar wiwi wasu abubuwa masu cutarwa, adda mai kaifi, wuƙa da kuma wasu abubuwa da ake kyautata zaton suna da alaƙa da ayyukan laifi.

Ana ci gaba da bincike don tantance waɗanda ake zargin ko suna da hannu a ayyukan laifi a cikin birnin da kuma gano waɗanda suke taimaka musu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga PantamiGazawar Demarketing: Yadda Sukar Rarara Mai Cike da Kiyayya ga Pantami Ya Rushe Daga Yushau A. ShuaibƘungiyar NARD ta yi Barazanar Shiga Yajin AikiDakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Ƴan Bindiga 3 Sun Ceto Mutane 9 da akai Garkuwa da suƳan Bindiga sun kai Hari a Kotun Shari'a da ke Jihar KatsinaBa ma Goyon Bayan a Riƙa Tura Sojoji Domin Aikin Tsaro a Lokacin Zaɓe - INECJam'iyyar NDC ta Buƙaci Sanata Hanga da Gaya da su Sake Tunani Kan Sauya SheƙaYan Bindiga Sun Kashe Kanal Abdussalam Ude Sun Raunata MatarsaMutane 15 Sun Mutu a Sabon Harin Yan Bindiga a Jihar Benue Zaɓen 2027: Uba Sani ya zaɓi Mataimakinsa
X whatsapp