Home SIYASA Abin da Obi ya Fada Kan Atiku – Dele Momodu

Abin da Obi ya Fada Kan Atiku – Dele Momodu

Momodu

Abin da Obi ya Fada Kan Atiku – Dele Momodu

 

Abuja – Daya daga cikin manya a jam’iyyar ADC, Dele Momodu, ya yi magana game da zaben shugaban kasa na 2027 a Najeriya.

Dele Momodu ya bayyana cewa Peter Obi ya taba kin amincewa da shawararsa ta hada kai da Atiku Abubakar a siyasa.

Abin da Obi ya fada kan Atiku Abubakar

Momodu ya ce Obi ya shaida masa cewa ya fi Atiku farin jini a tsakanin al’umma, cewar rahoton Punch.

Tsohon ‘dan takarar shugaban kasar ya bayyana cewa idan aka tambayi Obi, zai tabbatar bai yi masa karya ba ko kadan a kalamansa.

Momodu ya ce:

“Peter shi ne ɗan siyasa kaɗai da ya taɓa ziyartar gidana a London, Ghana da Lagos, a ɗaya daga cikin ziyarar, na gaya wa Peter cewa, ‘Ka yi ƙoƙarin yin aiki tare da Atiku.’

Momodu ya ce ya kawo misalin John Mahama na Ghana, wanda watakila da bai zama shugaban kasa ba da bai fara zama mataimakin Atta Mills ba.

Ya kuma kawo misalin Amurka, inda Joe Biden ya dawo ya zama shugaban kasa bayan ya nuna kwarewa duk da tsufansa.

“Na kuma ba shi misalin Amurka, inda duk da cewa Biden ya fi Obama shekaru sosai, amma daga baya ya dawo ya zama Shugaban Ƙasa saboda ya nuna ƙwarewa da cancantarsa.

“Kai dai ka taɓa zama gwamnan jiha ne kawai, amma Peter ya gaya mini cewa ya fi Atiku farin jini. Na rantse da Ubangiji. Idan ka gan shi, ka tambaye shi ko na yi masa ƙarya.”

A cewarsa, Obi ya taba zama gwamnan jiha ne kawai, amma ya dage yana ikirarin cewa ya fi Atiku karbuwa a idon jama’a, cewar Daily Post.

Momodu ya kuma yi tsokaci kan yanayin siyasar kasar, yana cewa akwai masu ruwa da tsaki da dama da ke fargabar karuwar tasirin Tinubu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp