Home Taska Hukumar EFCC ta Gurfanar da Ma’aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bn

Hukumar EFCC ta Gurfanar da Ma’aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bn

Awolegan Omolola Omotola,

Hukumar EFCC ta Gurfanar da Ma’aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bn

Ekiti – Hukumar EFCC ta gurfanar da wani da ke ikirarin shi boka ne, Olorunbukunmi Taiwo, tare da matarsa, Awolegan Omolola Omotola, kan zargin damfarar kudi da suka kusan Naira biliyan biyu.

An gurfanar da ma’auratan ne a gaban Mai shari’a Abubakar Usman na babbar kotun tarayya da ke zamanta a Ado-Ekiti bisa tuhume-tuhume shida.

Yadda EFCC ta kama miji da mata

Rahoton shari’ar da EFCC ta wallafa a shafinta na X ya nuna cewa tuhume tuhumen shida sun shafi damfara da boye kudaden da ake zargin an samu ta haramtacciyar hanya.

EFCC ta sanar da cewa ta kama wadanda ake zargin ne bayan wata mata mai makarantar kudi a jihar Delta, Anazia Colina Kenechukwu, ta shigar da korafi a kansu.

Matar ta bayyana cewa Taiwo ya tuntube ta yana neman ta ba shi kudin da zai yi amfani da su wajen gudanar da wata kwangilar gina hanya da ya ce hukumar DESOPADEC ta ba shi.

A cewarta, ta tura jimillar kudin da suka kai N1,980,000,000 zuwa asusun Taiwo da ke bankin Access Bank.

Sai dai binciken EFCC ya gano cewa an karkatar da kudaden wajen sayen kadarori biyu a Ado-Ekiti.

Kadarorin da EFCC ta kwace

Hukumar ta bayyana cewa ma’auratan sun sayi wani wurin shakatawa mai suna Town Tavern Lounge da wani gida mai dakuna hudu da kudaden da ake zargin an samu ta damfara.

An ce kadarorin suna yankin Ikere Road da Florence Court a Ado-Ekiti.

EFCC ta ce ta samu umarnin kotu a ranar 25 ga Mayu, 2026 domin karbe kadarorin na wucin gadi yayin da ake ci gaba da bincike.

Abin da tuhumar EFCC ta kunsa

Daya daga cikin tuhume-tuhumen ya nuna cewa ma’auratan sun karbi N1,098,961,500 daga hannun matar ta hanyar karya cewa za a yi amfani da kudin wajen gudanar da kwangilar gina hanya.

Ana zarginsu da aikata laifin da ya saba wa dokar damfara ta AFFOFRO ta shekarar 2006, kuma ma’auratan sun musanta aikata dukkan tuhume-tuhumen a lokacin da aka karanta musu a kotu.

Lauyan EFCC, Sesan Ola, ya roki kotu ta sanya ranar fara shari’a tare da bayar da umarnin tsare wadanda ake zargin.

Mai shari’a Abubakar Usman ya dage sauraron karar zuwa ranar Alhamis, 11 ga Yunin 2026, kuma ya bayar da umarnin a ci gaba da tsare ma’auratan a hannun EFCC har zuwa ranar da za a sake zama.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp