Home Taska Hukumar EFCC ta Gurfanar da Ma’aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bn

Hukumar EFCC ta Gurfanar da Ma’aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bn

Awolegan Omolola Omotola,

Hukumar EFCC ta Gurfanar da Ma’aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bn

Ekiti – Hukumar EFCC ta gurfanar da wani da ke ikirarin shi boka ne, Olorunbukunmi Taiwo, tare da matarsa, Awolegan Omolola Omotola, kan zargin damfarar kudi da suka kusan Naira biliyan biyu.

An gurfanar da ma’auratan ne a gaban Mai shari’a Abubakar Usman na babbar kotun tarayya da ke zamanta a Ado-Ekiti bisa tuhume-tuhume shida.

Yadda EFCC ta kama miji da mata

Rahoton shari’ar da EFCC ta wallafa a shafinta na X ya nuna cewa tuhume tuhumen shida sun shafi damfara da boye kudaden da ake zargin an samu ta haramtacciyar hanya.

EFCC ta sanar da cewa ta kama wadanda ake zargin ne bayan wata mata mai makarantar kudi a jihar Delta, Anazia Colina Kenechukwu, ta shigar da korafi a kansu.

Matar ta bayyana cewa Taiwo ya tuntube ta yana neman ta ba shi kudin da zai yi amfani da su wajen gudanar da wata kwangilar gina hanya da ya ce hukumar DESOPADEC ta ba shi.

A cewarta, ta tura jimillar kudin da suka kai N1,980,000,000 zuwa asusun Taiwo da ke bankin Access Bank.

Sai dai binciken EFCC ya gano cewa an karkatar da kudaden wajen sayen kadarori biyu a Ado-Ekiti.

Kadarorin da EFCC ta kwace

Hukumar ta bayyana cewa ma’auratan sun sayi wani wurin shakatawa mai suna Town Tavern Lounge da wani gida mai dakuna hudu da kudaden da ake zargin an samu ta damfara.

An ce kadarorin suna yankin Ikere Road da Florence Court a Ado-Ekiti.

EFCC ta ce ta samu umarnin kotu a ranar 25 ga Mayu, 2026 domin karbe kadarorin na wucin gadi yayin da ake ci gaba da bincike.

Abin da tuhumar EFCC ta kunsa

Daya daga cikin tuhume-tuhumen ya nuna cewa ma’auratan sun karbi N1,098,961,500 daga hannun matar ta hanyar karya cewa za a yi amfani da kudin wajen gudanar da kwangilar gina hanya.

Ana zarginsu da aikata laifin da ya saba wa dokar damfara ta AFFOFRO ta shekarar 2006, kuma ma’auratan sun musanta aikata dukkan tuhume-tuhumen a lokacin da aka karanta musu a kotu.

Lauyan EFCC, Sesan Ola, ya roki kotu ta sanya ranar fara shari’a tare da bayar da umarnin tsare wadanda ake zargin.

Mai shari’a Abubakar Usman ya dage sauraron karar zuwa ranar Alhamis, 11 ga Yunin 2026, kuma ya bayar da umarnin a ci gaba da tsare ma’auratan a hannun EFCC har zuwa ranar da za a sake zama.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp