Home Labarai Fiye da Kashi 60 na ‘Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin...

Fiye da Kashi 60 na ‘Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara – IMF

IMF

Fiye da Kashi 60 na ‘Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara – IMF

 

Asusun Lamuni na Duniya ya ce garambawul ɗin da gwamnatin Najeriya ta aiwatar ya ƙarfafa tattalin arziƙin ƙasar, amma ya yi gargaɗin cewa fiye da kashi 60 na ‘yan Najeriya a yanzu suna rayuwa cikiin fatara.

Tun bayan hawansa kan mulki shekara uku da ta wuce, Shugaba Bola Tinubu ya cire tallafin man fetur mai tsada wanda ya sa tsawon shekaru gommai ‘yan ƙasar ke shan man fetur da arha, sannan ya sassauta tsarin canjin kuɗi ga naira kuma ya yi wa harkar karɓar harajin Najeriya gyaran fuska.

Kamfanin dillancin labarai na AFP ya ruwaito IMF na cewa yayin da masana tattalin arziƙi ke cewa ya dace a kawo manufar sauye-sauyen tun da daɗewa, amma talauci ya ci gaba da ƙaruwa, inda a ƙarshen shekara ta 2025 yake addabar kashi 63 na al’ummar Najeriya.

Kuma sama da mutum miliyan 27 ne ke fama da rashin wadatar abinci a shekarar, in ji IMF.

A cikin wata sanarwa bayan bitar tattalin arziƙin najeriya na shekara-shekara, IMF ya ce: “Har yanzu halin rayuwa ya kasance mai wahala ga ‘yan Najeriya masu yawa”.

Ya ce talauci na ƙaruwa a ƙasar mafi yawan jama’a a Afirka tsawon shekaru, inda rahoton Babban Bankin Duniya na baya-bayan nan ya ce ‘yan Najeriya kimanin kashi 61 ne ke rayuwa cikin talauci, sama daga kashi 40 na adadinsu a 2019.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban JosMatsalar Tsaro:  An Kashe Manoma 6 a Jihar Kaduna An Zargi Kwankwaso da Sayen Fom ɗin Takara na Kujeru 69 a Jam'iyyar PRPƘasurgumin ɗan bindiga, Turji ya ɗauki Alhakin Kashe Sojoji a Jihar SokotoMasu Iƙirarin Jihadi Sun Hallaka Manoma 11 a Jihar Borno 'Yan Bindiga sun ƙone shingen Jami'an NSCDC Tare da Garkuwa da Mutum 1 a Jihar KebbiTaron NUJ: Lokacin Da Manyan Jami’an Tsaro Suka Guji Yan Jarida Daga Yushau A. ShuaibSamar da Tsaro: Sojojin Najeriya sun Kama ƴan ƙasashen Wajen 46Ta'addanci: Za a Gurfanar da Mutane 400 a Gaban Kotun Tarayya da ke AbujaAn Ceto Matar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaHauhawar Farashin Kayan Masarufi a Najeriya ya ƙaru Zuwa Kashi 15.93Rundunar Sojin Najeriya ta Gudanar da Hare-Hare Kan Maɓoyar ƴan Bindiga a Jihar Katsina
X whatsapp