Home Labarai Fiye da Kashi 60 na ‘Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin...

Fiye da Kashi 60 na ‘Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara – IMF

IMF

Fiye da Kashi 60 na ‘Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara – IMF

 

Asusun Lamuni na Duniya ya ce garambawul ɗin da gwamnatin Najeriya ta aiwatar ya ƙarfafa tattalin arziƙin ƙasar, amma ya yi gargaɗin cewa fiye da kashi 60 na ‘yan Najeriya a yanzu suna rayuwa cikiin fatara.

Tun bayan hawansa kan mulki shekara uku da ta wuce, Shugaba Bola Tinubu ya cire tallafin man fetur mai tsada wanda ya sa tsawon shekaru gommai ‘yan ƙasar ke shan man fetur da arha, sannan ya sassauta tsarin canjin kuɗi ga naira kuma ya yi wa harkar karɓar harajin Najeriya gyaran fuska.

Kamfanin dillancin labarai na AFP ya ruwaito IMF na cewa yayin da masana tattalin arziƙi ke cewa ya dace a kawo manufar sauye-sauyen tun da daɗewa, amma talauci ya ci gaba da ƙaruwa, inda a ƙarshen shekara ta 2025 yake addabar kashi 63 na al’ummar Najeriya.

Kuma sama da mutum miliyan 27 ne ke fama da rashin wadatar abinci a shekarar, in ji IMF.

A cikin wata sanarwa bayan bitar tattalin arziƙin najeriya na shekara-shekara, IMF ya ce: “Har yanzu halin rayuwa ya kasance mai wahala ga ‘yan Najeriya masu yawa”.

Ya ce talauci na ƙaruwa a ƙasar mafi yawan jama’a a Afirka tsawon shekaru, inda rahoton Babban Bankin Duniya na baya-bayan nan ya ce ‘yan Najeriya kimanin kashi 61 ne ke rayuwa cikin talauci, sama daga kashi 40 na adadinsu a 2019.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a Kano
X whatsapp