Home Labarai Fiye da Kashi 60 na ‘Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin...

Fiye da Kashi 60 na ‘Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara – IMF

IMF

Fiye da Kashi 60 na ‘Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara – IMF

 

Asusun Lamuni na Duniya ya ce garambawul ɗin da gwamnatin Najeriya ta aiwatar ya ƙarfafa tattalin arziƙin ƙasar, amma ya yi gargaɗin cewa fiye da kashi 60 na ‘yan Najeriya a yanzu suna rayuwa cikiin fatara.

Tun bayan hawansa kan mulki shekara uku da ta wuce, Shugaba Bola Tinubu ya cire tallafin man fetur mai tsada wanda ya sa tsawon shekaru gommai ‘yan ƙasar ke shan man fetur da arha, sannan ya sassauta tsarin canjin kuɗi ga naira kuma ya yi wa harkar karɓar harajin Najeriya gyaran fuska.

Kamfanin dillancin labarai na AFP ya ruwaito IMF na cewa yayin da masana tattalin arziƙi ke cewa ya dace a kawo manufar sauye-sauyen tun da daɗewa, amma talauci ya ci gaba da ƙaruwa, inda a ƙarshen shekara ta 2025 yake addabar kashi 63 na al’ummar Najeriya.

Kuma sama da mutum miliyan 27 ne ke fama da rashin wadatar abinci a shekarar, in ji IMF.

A cikin wata sanarwa bayan bitar tattalin arziƙin najeriya na shekara-shekara, IMF ya ce: “Har yanzu halin rayuwa ya kasance mai wahala ga ‘yan Najeriya masu yawa”.

Ya ce talauci na ƙaruwa a ƙasar mafi yawan jama’a a Afirka tsawon shekaru, inda rahoton Babban Bankin Duniya na baya-bayan nan ya ce ‘yan Najeriya kimanin kashi 61 ne ke rayuwa cikin talauci, sama daga kashi 40 na adadinsu a 2019.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp