Home Labarai Gwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi...

Gwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasarta

Biance Ojukwu

Gwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasarta

 

Najeriya ta ce tana nazarin matakan da za ta ɗauka kan Afrika ta Kudu, bayan samun rahotannin kai hare-hare kan ƴan ƙasarta da take shirin fara kwashe su a gobe Laraba.

Ministar harkokin wajen Najeriyar Bianca Ojukwu ta ce gwamnatin ƙasar na duba yiwuwar mayar da martani kan abin da ke faruwa.

Ministar ta ce duk da yake wannan matakin abu ne da za a cimma matsaya kansa nan gaba, amma ana ci gaba da tattaunawa kan abin da ya dace a yi.

Ta zargi hukumomin Afrika ta Kudu da gaza yin komai kan hare-haren da ƴan ƙasarta ke kaiwa Ƴan Najeriya, inda ministar ta ce yawancin waɗanda ke zaune a can suna da takardu kuma sun cika duk wasu ƙa’idojin da suka kamata.

Bianca ta ce sun samu bayanan yadda aka wawushe shagunan ƴan Najeriya da ke sana’o’insu a ƙasar, wasu kuma an cinna wa shagunan nasu wuta tare da haramtawa yaransu zuwa makaranta saboda yadda ake cin zarafinsu.

Ta caccaki gwamnatin Afrika ta Kudu kan yadda har yanzu ba ta fito fili ta yi bayani da kakkausar murya ko ta ɗauki tsattsauran mataki kan abi da ke faruwa ba.

Ministar ta ƙara da cewa Najeriya ba ta ji daɗin hakan ba, ganin yadda ta ba Afrika ta Kudu gudummuwa sosai wajen gwagwarmayar yaki da wariyar launin fata a ƙasar.

Kalama nata na zuwa ne a daidai lokacin da ƴan ci rani ke ci gaba da zaman ɗarɗar a Afrika ta Kudu, inda ƴan ƙasar ke yin zanga-zangar ƙyamar baƙi da kuma buƙatar ƴan kama wuri zauna su bar ƙasar nan da 30 ga watan Yuni.

Shugaban Afrika ta Kudu Cyril Ramaphosa ya sanar da wasu matakai da ƙasar ke ɗauka wajen daƙile kwararar baƙin haure.

Sai dai kuma ya gargaɗi ƴan ƙasarsa da su guji ɗaukar doka a hannunsu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp